Connect with us

Labarai

Masu masana’antu sun amince da ƙaddamar da katin lamunin kuɗin dala a Najeriya

Published

on

Kwana biyu bayan ƙaddamar da katin lamuni na kuɗin dala a Najeriya, wato American Express Credit Card, irinsa na farko a Afrika, masana tattalin arziƙi sun fayyace bambancinsa da kuɗin Crypto, yayin da masu masana’antu ke cewa, akwai buƙatar wayar da kan ‘yan kasuwa akan alfanun aiki da katin.

A ranar Alhamis ne kamfanin American Express ya ƙaddamar da katin lamuni na kuɗin dala a birnin Legas, a wani mataki na sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya musamman ‘yan kasuwa a harkokinsu da ke da alaƙa da kuɗaɗen ƙetare na dala.

Dakta Lawan Habib Yahya, masanin tattalin arziƙi ne a Najeriya, ya yi ƙarin bayani dangane da alaƙar wannan katin na lamunin kuɗin dala da kuma darajar takardun kuɗin Najeriya na Naira.

“Idan buƙatun neman musayar kuɗaɗen ƙetare na dala suka ragu daga kamfanoni da ɗaiɗaikun mutane, saboda suna samun waɗannan kuɗaɗen ta hanyar katin lamuni daga kamfanin American Express Credit Card, to babu shakka darajar naira na iya ƙaruwa saboda dama yawaitar buƙatun kuɗin dalar ne ke daga farashinta,” a cewar Dakta Lawan.

Da alama dai masu masana’antu a Najeriya sun yi maraba da wannan yunƙuri na ƙaddamar da katin lamuni na kuɗin dala a Najeriya, kamar yadda Alhaji Sani Hussaini Sale, mamba a kwamitin ƙoli na ƙungiyar masu masana’antu ta Najeriya (MAN), kuma mataimakin shugaban cibiyar kula da harkokin kasuwanci, masana’antu, ma’adinai, da ayyukan noma ta jihar Kano (KACCIMA) ya bayyana.

“Dama kokawar cinikayya da ƙasashen waje ta zama da wahala saboda dalar na neman ta tada hankali, amma zuwan wannan tsari na katin ba da lamuni na kuɗin dala zai magance ƙalubalen, musamman yadda idan aka ba ka kuɗi daga dala dubu ɗaya zuwa dubu 20 za su taimaka sosai, a cewar Alhaji Sani.

KU KUMA KARANTA:Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Ya kuma ce “Fatan mu shi ne wannan kamfani na American Express credit Card ya iso Kano a arewacin Najeriya, don mu haɗa hannu da shi a cibiyarmu. Zamu sada shi da ‘yan kasuwa domin wayar da kansu game da alfanun wannan tsari da ya zo da shi”.

Amma a cewar, Dakta Lawan Habib Yahya, akwai bambanci a tsakanin katin lamuni na American Express Credit Card da kuɗaɗen Crypto da ake hada-hadarsu a kafar zamani ta Intanet.

“Shi kuɗin Crypto kuɗi ne da ake juya shi ta kafar sadarwa ta Intanet, ba kuɗi ne lakadan ba, amma shi American Express Credit Card kudi ne lakadan za’a saka maka a katinka kuma ka yi sayayya ko cinikayya da shi a kasashen waje, kamar yadda za ka yi amfani da katinka na bankin Najeriya takardun kuɗi na naira su fita,” inji Dakta Lawan.

Baya ga Najeriya, kamfanin American Express ya ce yana da burin faɗaɗa wannan tsari na katin lamunin kuɗin dala zuwa sauran ƙasashen Afrika kamar su Rwanda da Ghana.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Published

on

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

 

Tinubu ya naɗa sabbin sakatarorin dindindin

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗin sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya guda takwas da za su cike guraben da ake da su a wasu jihohi da shiyyoyin ƙasar a ma’aikatan gwamnati.

Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da bayanai ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a jiya Juma’a, inda ya ce an naɗa sabbin sakatarorin dindindin ɗin ne bayan da ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya gudanar da aikin zaɓo su.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Sakatarorin su ne: Dr Emanso Umobong Okop – Akwa-Ibom, Obi Emeka Vitalis – Anambra, Mahmood Fatima Sugra Tabi’a – Bauchi, Danjuma Mohammed Sanusi – Jigawa, Olusanya Olubunmi – Ondo, Dr Keshinro Maryam Ismaila – Zamfara, Akujobi Chinyere Ijeoma (Kudu-maso-Gabas)) da kuma Isokpunwu Christopher Osaruwamwen (Kudu-maso-Kudu).

“Shugaban ya yi hasashen cewa sabbin sakatarorin dindindin na gwamnatin tarayya za su yi aiki da ƙwazo, himma da riƙon amana ga ƙasa wajen gudanar da ayyukansu tare da tabbatar da ingantacciyar hidima ga al’ummar Najeriya,” in ji sanarwar.

Continue Reading

Labarai

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Published

on

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

 

Tinubu ya amince da raba Naira dubu 50 ga iyalai miliyan 3.6 na tsawon watanni 3

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ba da Naira dubu hamsin-hamsin ga iyalai miliyan 3.6 har tsawon wata uku a faɗin Nijeriya.

Wannan na ɗaya daga cikin yarjejeniyoyi da aka cimma a ganawar da Tinubu ya yi da gwamnonin jihohi 36 na ƙasar nan a yau Alhamis a Abuja.

Shugaban ya ba da umarnin raba kuɗin ga iyalai dubu 100 a kowace jiha har na tsawon watanni uku.

Sauran batutuwa da aka cimma a ganawar sun haɗa da:

* Bawa iyalai 100,000 a kowace jiha tallafin N50,000 na tsahon wata uku.

* Ware Naira biliyan 155 domin siyen kayan abinci da za a tallafawa masu ƙaramin ƙarfi kan farashi mai rahusa.

* Baiwa kowace jiha Naira biliyan 10 domin sayen motocin sufuri masu aiki da iska gas domin sauko da farashin kuɗin zirga-zirga.

KU KUMA KARANTA:Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

* Gaggauta fara aikin hanyar da ta tashi daga Sakkwato zuwa Badagary a Lagos. Hanyar zata ratsa ƙauyuka kimanin 216, madatsun ruwa (dams) guda 58, ƙananan hukumomi 156 da manyan garuruwa 39 da kuma gonaki da suka kai kimanin hectare miliyan ɗaya. Titin zai ratsa jihohin Sokoto da Kebbi da Niger da Kwara da Oyo da Ogun da kuma Lagos.

* Shugaba Tinubu ya kuma amince da biyan kuɗin aikin hanyar jirgin ƙasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri wadda za ta ratsa jihohin Rivers da Abia da Enugu da Benue da Nasarawa da Plateau da Bauchi da Gombe da Yobe da kuma Borno.

* Haka nan an amince da biyan kuɗin da ake buƙatar domin yin aikin hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Ibadan zuwa Abuja a wani ɓangare na aikin dogo da ya tashi daga Lagos zuwa Kano. Aikin zai haɗa jihohin Lagos da Ogun da Oyo da Osun da Kwara da Niger da Abuja da Kaduna da kuma Kano.

* Shugaban ƙasa ya kuma bada umarnin cigaba da aikin hanyar Lagos zuwa Calabar wadda kuma zata yi rassa a jihohin Benue da Kogi da Abuja da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Published

on

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin Kano ta mayar da martani kan ɗaga tuta a fadar Nasarawa

Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da batun ɗaga tutar masarauta da aka yi a gidan sarki na Nassarawa wurin da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ke zaune, inda ta bayyana hakan da ƙoƙarin jan hankalin jama’a kawai.

Tutar, wata alama ce ta iko dake nuni da cewar Sarki na nan, a kullum ana ɗaga ta da misalin ƙarfe 6 na safe a kuma sauƙe ta da misalin ƙarfe 6 na yamma. Duk lokacin da sarki ba ya cikin fada ko ya yi balaguro za ta kasance a sauƙe.

Da safiyar ranar Alhamis, aka lura cewar an ɗaga tutar da misalin ƙarfe 6 na safiya a fadar Nassarawa, abin da ya haifar da kace-nace dama raɗe-raɗi.

Kowane daga cikin Aminu Ado Bayero da Muhammadu Sanusi II na iƙirarin shi ne Sarkin Kano kuma suna ci gaba da aiwatar da ayyukan sarauta.

KU KUMA KARANTA:An sauya Kwamishinan ’yan sandan Kano

Gwamnatin jihar ce ta sauƙe Aminu Ado Bayero tare da sake naɗa Muhammadu Sanusi biyo bayan yiwa dokar masarautu ta Kano kwaskwarima.

An ɗaga irin wannan tuta a fadar gidan Rumfa, inda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ke zaune.

Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya yi fatali da batun ɗaga tuta a fadar Nassarawar, inda yace hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma.

Ya shaidawa manema labarai cewar, “hakan wani yunƙuri ne na jan hankalin al’umma. Amma babu shakku ko tantamar cewar Sanusi ne Sarkin Kano.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like