Connect with us

Labarai

Lagos za ta ƙaddamar da jirgin ƙasa mai zirga-zirga a cikin gari

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnatin jihar Lagos ta sanar da cewa rukunin farko na sufurin jirgin ƙasa da zai yi zirga-zirga a cikin birnin Ikko mai taken Blue Rail Line zai fara aiki ranar Litinin 4 ga watan Satumba.

Manajar darakta a hukumar kula da sufuri a ƙwaryar birnin Lagos (LAMATA), Misis Abimbola Akinajo ce ta sanar da haka a tashar jirgin ƙasa ta Marina ranar Laraba, inda ta nunar cewa jirgin farko zai tashi ne da misalin ƙarfe 9 na safe, inda Gwamna Babajide Sanwo-Olu zai kasance a cikin jirgin tare da sauran fasinjoji daga Marina zuwa tashar Mile 2.

Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin jihar Lagos ta gayyaci ‘yan jarida waɗanda suka zagaya a cikin jirgin ƙasa mai suna Lagosmetro.

Misis Abimbola Akinajo ta bayyana cewa a cikin mako huɗu na farko jirgin ƙasa mai amfani da kwal zai riƙa zirga-zirga tsawon sa’a 12.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sandan Legas sun kama wasu da ake zargi da ɓarnata titin jirgin kasa

Daga nan kuma sai jirage masu tafiya da lantarki su fara aiki da jigila 76, kuma an yi ƙiyasin cewa jiragen ƙasa za su riƙa ɗaukar fasinjoji tsakanin 150,000 ko 175,000 a kullum yaumin.

Jiragen ƙasa za su riƙa sufuri ne tun daga ƙarfe 5:30 na safe har zuwa ƙarfe 11 na dare.

Misis Abimbola Akinajo ta ce jirgin ƙasan zai riƙa tsayawa ne tsawon minti ɗaya da rabi kawai a kowacce tasha.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Gwamnati za ta rufe tashar jirgin saman Legas | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gwamnati za ta rufe tashar jirgin saman Legas - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Published

on

ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro - Badaru

ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma ECOWAS tana buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don samar da ƙaƙƙarfar rundunar tsaro da za ta yi yaƙi da ta’addanci, a cewar ɗaya daga cikin zaɓuka biyun da hukumomin tsaro na ƙasashen yankin ke duba yiwuwarsu a taron da suka yi a jiya Alhamis.

Ministocin Tsaro da na Kuɗi na Ƙasashen ECOWAS sun yi taron a Abuja, babban birnin Najeriya, inda suka tattauna kan yanke shawarar yawan dakarun da kuma yawan kuɗaɗen da ake buƙata don samar da ita.

Afirka ta Yamma na fama da matsalolin juyin mulki, lamarin da yake zama matsala ga tsarin siyasa da jawo rarrabuwar kai tsakanin ƙasashen yankin.

KU KUMA KARANTA: Masana sun yi ƙira da a yi sabbin sauye-sauye ECOWAS

A watan Janairu, shugabannin mulkin soji na Nijar da Burkina Faso da Mali sun yanke shawarar ficewa daga ƙungiyar mai mambobin ƙasashe 15.

Ministan Tsaron Najeriya ya shaida wa taron cewa akwai zaɓi biyu a samar da rundunar yankin: Daya za a kashe dala biliyan 2.6 duk shekara a kan runduna mai dakaru 5,000, dayan kuma za a kashe dala miliyan 481 a dakaru 1,500
“Waɗannan alkaluma sun nuna muhimmancin aikin da ke gabanmu,” in ji Badaru.
“Don haka ya zama wajibi mu yi nazari sosai kan zabin duba da irin kalubalen da yankinmu ke fuskanta a halin yanzu da kuma matsalolin kudi da kasashe mambobinmu ke fuskanta.”

Tun a shekarar 2020, sojoji a kasashen uku suka yi juyin mulki suna zargin shugabannin farar hula da ƙyale masu da’awar jihadi su samu galaba.

Da hawansu kan mulki, sojojin sun yi watsi da yarjejeniyoyin tsaro da aka ƙulla da sojojin Amurka da Faransa da kuma na Majalisar Dinkin Duniya tare da gayyatar Rasha da su maye gurbinsu.

Ministan Tsaron Nijeriya ya kara da cewa ba za a yi amfani da rundunar yankin wajen ɗaukar mataki a kan juyin mulkin ba, illa kawai yaƙi da ta’addanci. Ana sa ran kowace ƙasa mamba za ta ba da gudunmawar wani kaso, in ji shi.

Shugaban hukumar ECOWAS Omar Touray ya ce ba za a cire mambobin da aka dakatar daga cikin rundunar yankin ba.

“An yi imanin ba za mu iya yaki da ta’addanci mu kadai idan har wasu ba su shiga ba,” in ji Touray.

“Ko da yake ana iya dakatar da wasu kasashe amma ya kamata a bar su su shiga tarukan da suka shafi tsaro, shi ya sa muka gayyaci dukkan kasashe mambobi 15 da su halarci wannan muhimmin taro.”

Continue Reading

Labarai

Saudiyya na son fara shigar da naman shanu da waken suya ƙasarta daga Najeriya

Published

on

Saudiyya na son fara shigar da naman shanu da waken suya ƙasarta daga Najeriya

Saudiyya na son fara shigar da naman shanu da waken suya ƙasarta daga Najeriya

Ministan Harkokin Noma na Najeriya Mohammad Abubakar ya ce Saudiyya ta nuna sha’awar fara shigar da ton 200,000 na naman shanu da ton miliyan ɗaya na waken suya cikin ƙasarta duk shekara daga Najeriya.

Minista Mohammed ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis a Abuja cewa Saudiyya ta nuna sha’awar hakan ne bayan da Ministanta na Harkokin Noma ya ziyarci Najeriya tare da yin wasu taruka da ‘yan kasuwa a fannonin noma.

“Nuna sha’awar tasu kan wannan batu ke da wuya sai muka fitar da wani tsari da za mu iya samar da yawan abin da suke so da kuma biya musu buƙatarsu,” a cewar Ministan Harkokin Noman na Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Masu sana’ar sayar da tumatur sun yi barazanar daina kai wa jihar Legas

Ya ƙara da cewa dama Najeriya na neman abokan hulɗa na kasuwanci don samun kuɗaɗen ƙasashen waje bayan da ta sha fama da ƙarancin dalar Amurka, lamarin da ya yi mummunar illa kan tattalin arzikinta da kuma rage darajar kudin ƙasar na Naira sosai.

Najeriya ta daɗe tana son raba ƙafa kan harkokin fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje, maimakon fitar da ɗanyen man fetur kawai, wanda a yanzu fitar da shi shi kaɗai ba ya iya riƙe tattalin arzikinta sosai.

Continue Reading

Labarai

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Published

on

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Daga Muhammad Kukuri

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya ɗaga tutar mulki a ƙaramar fadar da ke unguwar Nassarawa inda yake zaune.

A bisa al’ada, tutar na zama ne a matsayin alamar iko, kuma daga ta na alamta cewa sarki yana cikin fada.

Wannan kuwa na zuwa ne duk da umarnin gwamnatin Kano ga Sarki Aminu ya fice daga fadar a yayin da ake ci gaba da dambarwar sarautar Kano.

Akan daga tutar ce da misalin karfe 6 na safe a kuma sauke ta 6 na yamma ko idan sarki ya yi bulaguron aiki.

Neptune Prime Hausa ta gano cewa ba a ɗaga tutar ba a Fadar Nassarawa ba sai a safiyar Alhamis, duk da cewa an sanya karfenta a safiyar Laraba.

An yi ta ji-ta-ji-ta ranar Laraba cewa an sanya tutar, amma mun gano cewa kafen kawai aka sa, Alhamis da safe kuma aka daga tutar.

Daga tutar a karamar Fadar Nassarawa na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da shari’ar da Gwamnatin Kano ke neman kotu ta hana Aminu Ado Bayero Aminu gabatar da kansa a matsayin Sarkin Kano bayan ta maye gurbinsa sa Muhammadu Sanuni II, Sarkin Kano na 16.

Gwamnatin jihar ta je kotu ne tana neman a hana duk sarakuna biyar da ta rushe masarautunsu a jihar gabatar da kansu a matsayin sarakunan masarautun.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like