Connect with us

'Yansanda

Jami’an ‘yan sanda sun cafke dattijuwa da ta sace yara 3 a Borno

Published

on

Wata mata ‘yar Kimanin shekaru 60, mai suna Nsa Heneswa da ake zargi da safarar mutane ta shiga hannun ‘yan sanda a birnin Maiduguri na jihar Borno. An kamata ne tare da Almajirai biyu, da yarinya ‘yar shekara biyu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abdu Umar ne ya bayyana haka a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a Maiduguri. Ya ce an kama wadda ake zargin ne a tashar mota ta Borno Express ranar 4 ga watan Agusta. Umar ya ce wadda ake zargin ta shiga Maiduguri ne a ranar 3 ga watan Agusta, inda ta je kai tsaye kasuwar Litinin inda ta ga wasu yara marasa galihu da aka fi sani da “Almajiri” suna bara a hanya.

A cewarsa, wadda ake zargin ta kira ɗaya daga cikin yaran ne ta ba shi Naira 200 sannan ta nemi ya raka ta domin ta saya masa kaya.

Daga nan sai ta koma cikin garin domin neman wani yaron,” inji shi. Umar ya ce wanda ake zargin ta isa unguwar Yan’ Nono da ke unguwar Bulumkutu inda ta yi awon gaba da wani yaro na Misis Amina Ayuba, wata mai sana’ar sayar da nono.

“Lokacin da ta isa tashar mota, ta nemi motar da za ta je Legas amma ‘yan kungiyar sun shaida mata cewa tuni ta tashi. “Sai ta nemi wurin zama kafin gobe. “Sai ta ƙara fita ta ɗauki ɗa na uku, sai dubunta ya cika, sa’a ta ƙare mata lokacin da ta yanke shawarar kai ɗaya daga cikin yaran gidan cin abinci,” in ji shi.

CP ya ce wani direba ne da ke aiki a layin Abuja a tashar motocin yayi shakku kan matar, yadda yaga tana abu kamar mara gaskiya, inda ya sanar da jami’an tsaro da su sa ido da tsaro a tashar motar.

Ya ce an kama wadda ake zargin tare da miƙa ta ga ‘yan sanda domin gudanar da bincike. Tana shirin kai yaran Legas. Umar ya ce mai yiwuwa wadda ake zargin tare da wadanda ke da hannu a cikinta sun daɗe suna sana’ar saye da sayar da yara kafin doka ta kama ta.

Da take magana da NAN a hannun ‘yan sanda, ta ce: “A gaskiya, wannan shine karo na farko da nake yin hakan. “Ban taɓa yin haka ba. Wata mata ce a Legas ta gabatar da ni ga wannan sana’a. “Ina kuma da wata ma’aikaciyar jinya da ke taimaka min a asibitin kwararru na Maiduguri,” in ji ta.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like