Connect with us

Labarai

Hukumar NEMA ta rarraba kayayyakin agaji ga waɗanda ambaliyar ruwa ya shafa a Kaduna

Published

on

Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta fara raba kayan agaji ga waɗanda bala’in ambaliyar ruwa ya rutsa da su da kuma sauran marasa galihu a jihar Kaduna bisa manufar bayar da agajin gaggawa na musamman na tattalin arziƙi da rayuwa (SNELEI).

Darakta Janar na Hukumar NEMA Mustapha Habib Ahmed wanda ya ƙaddamar da rabon kayayyakin a Kaduna a jiya, ya ce gwamnatin tarayya ta amince da ɗaukar matakin ne musamman ga mutanen da bala’in ambaliyan ruwa ya shafa a shekarar 2022 da kuma waɗanda aka bayyana a matsayin waɗanda suka fi kowa rauni a faɗin ƙasar nan.

Ahmed wanda ya samu wakilcin shugaban hukumar NEMA a shiyyar Kudu maso Gabas, Ngozi Echeazu, ta ce an tantance gidaje 660,884 da aka yi niyya don cin gajiyar tallafin na musamman a faɗin jihohi 36 da babban birnin tarayya (FCT).

Ya ce an ba wa manoma kayayyakin amfanin gona irin su tsiron amfanin gona da kayan aiki, suna ba manoma damar koma wa gonakinsu, da ƙarfafa noman amfanin gona da kuma kare lafiyar abinci na ƙasa, ya ƙara da cewa, ana sa ran shiga tsakani zai zaburar da ayyukan sarƙaƙiya tun daga tushe.

KU KUMA KARANTA: NEMA ta ba da tallafin kayan agaji ga mutane dubu 23 a Nijar

Ya ci gaba da cewa, kayayyakin tallafin an yi su ne domin a taimaka wa masu sana’o’in hannu wajen inganta sana’arsu da bunƙasa tattalin arziƙinsu.

Ya buƙaci waɗanda suka ci gajiyar tallafin da ka da su lalata kyakkyawar niyyar gwamnatin tarayya ta hanyar sayar da kayayyakin. Kayayyakin da aka raba sun haɗa da shinkafa, masara, dawa, ɗinki da injin niƙa.

Mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dakta Hadiza Balarabe, ta ce matakin abin a yaba ne matuƙa.

Wanda ya samu wakilcin mataimakin shugaban ma’aikata a ofishinta, Barista James Kanyip, ta ce; “Abin farin ciki a nan shi ne haɗin gwiwa tsakanin NEMA, SEMA da sauran hukumomi da gwamnatin jihar.

Hakan na nuni da cewa akwai alaƙa mai ƙarfi idan ana maganar magance bala’o’i da kuma samar da kayayyakin agaji ga waɗanda abin ya shafa ta irin wannan matakin.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like