Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara ta bai wa Matawalle wa’adin mayar da motocin alfarma na biliyoyin nairori

Published

on

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta bai wa tsohon gwamnan jihar Muhammad Bello Matawalle wa’adin kwanaki biyar da ya bayar da bahasi kan motocin alfarma na biliyoyin nairori da aka sayo daga susun gwamnatin jihar, kuma suka yi ɓatan-dabo.

A cikin wata sanarwa da babban mai taimaka wa gwamnan jihar kan harkokin yaɗa labarai Sulaiman Bala Idris ya fitar ya ce sabuwar gwamnati ta samu hujja da alaƙaluman kuɗin da aka ware wajen sayo wasu manyan motocin alfarma.

Sanarwar ta ce gwamnatin jihar ta samu hujja mai ƙarfi da ke nuna cewa tsohon gwamnan ya ware biliyoyin nairori wajen sayo manyan motocin alfarma da gwamnati za ta yi amfani da su.

KU KUMA KARANTA: Matawalle ya wawure motoci 17, injinan gas, da na’urorin talabijin na jami’an gwamnati – Gwamna Dauda

Sai dai sanarwar ta ce sabuwar gwamnati ba ta samu ko da mota guda cikin motocin da tsohuwar gwamnatin ta ce ta sayo ba, kamar yadda bayanai suka nuna.

A baya-bayan nan dai tsohon gwamnan na ta samun taƙun-saƙa da hukumar yaƙi da cin hanci da rasha EFCC bayan da ya zargi shugaban hukumar Abdurrasheed Bawa da aikata almundaha iri-iri.

A cikin wata sanarwa da EFCC ta fitar cikin makonni da suka gabata, ta ce tana bincikar gwamna Matawalle ne kan zargin karkatar da Naira biliyan 70, da bayar da kwangiloli ba bisa ƙa’ida ba.

“Kuɗin wanda aka samu a matsayin bashi daga wani banki domin aiwatar da ayyuka a sassan ƙananan hukumomin jihar, ana zargin gwamnan ya karkatar da shi ne,” kamar yadda sanarwar EFCCn ta bayyana.

A martanin da ya mayar tsohon gwamnan ya ƙalubalanci Bawa da ya sauka daga kan kujerarsa ya bayar da damar a bincike shi ya ga irin abubuwan da za a bankaɗo.

Cikin wata hira da ya yi da BBC Matawalle ya ce “Bincike gaskiya ne, ba a hana a yi bincike ba, amma kuma ya kamata binciken ya zamo na kowa da kowa, don bai kamata a ce komai sai dai a ambaci gwamna ba, ai ba gwamna ne kaɗai ke da asusun ajiya ba.”

Ya ce, “Kamar yadda shugaban EFCC ya ce ya tanadi takardu na gwamnoni, to muna so ya nuna wa duniya takardu na waɗanda yake aiki tare da su, sannan shi kansa ya kamata ya rubuta wa kansa takarda don a bincike shi saboda akwai zarge-zarge masu ɗimbin yawa a kansa.”

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: ‘Yan sanda sun mamaye gidan Matawalle, sun ƙwato motoci sama da 40 | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: ‘Yan sanda a Zamfara sun bi umarnin kotu, sun mayar wa da tsohon Gwamna Motocin sa | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like