Connect with us

Gobara

Gobara ta ɓarke a kotun ƙoli a Abuja

Published

on

A halin yanzu an samu tashin gobara a kotun ƙoli da ke babban birnin tarayya Abuja.

Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto ba a san musabbabin tashin gobarar ba, sai dai wata majiya daga hukumar kashe gobara ta tarayya ta ce jami’an kashe gobara na nan a wajen.

An ce an ƙona ofisoshin alƙalai uku. A cewar kafar yaɗa labarai ta ARISE, gobarar ta tilastawa wasu mutanen da ke cikin ginin yin tururuwa domin tsira da rayukansu.

KU KUMA KARANTA: Sakamakon Gobara: Hukumar wutar lantarki a Kebbi, ta yi asarar taransifoma na dala miliyan huɗu

Lamarin gobarar dai ita ce ta baya-bayan nan da ta shafi ofisoshin gwamnati a Abuja.

A watan Mayun 2023, gobara ta ƙone wasu sassan sansanin sojojin saman Najeriya dake kan titin filin jirgin sama a babban birnin tarayya Abuja.

A watan Fabrairun 2022, an samu gobara a ginin ma’aikatar kuɗi da ke Abuja.

A watan Mayun 2020, gobara ta ƙone wani ɓangare na ginin hukumar gidan waya ta Najeriya (NIPOST) a babban birnin tarayya Abuja. Wata guda gabanin faruwar lamarin, gobara ta ƙone wani gini dake ɗauke da ofishin akanta janar na tarayya.

A shekarar 2018, Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya (FFS) ta ce Najeriya ta yi asarar kimanin Naira Tiriliyan 5 sakamakon gobarar da ta faru cikin shekaru huɗu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Gobara

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Published

on

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa saƙon jajensa ga ‘yan kasuwar da shaguna da dukiyoyinsu suka ƙone a gobarar da ta tashi a kasuwar Karu a daren Alhamis.

Sanarwar da hadimin shugaban ƙasar akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngilale ya fitar a ranar Juma’a ta ce, shugaban ƙasar ya yi takaicin samun labarin gobarar da ta shafi wani sashe na kasuwar.

Da yammacin ranar Alhamis, gobara ta laƙume wani yanki na kasuwar, inda ta lalata ɗimbim dukiya da sauran kayayyaki masu daraja.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Sanarwar ta ƙara da cewar, shugaban ƙasa na miƙa saƙon jajensa ga ilahirin ‘yan kasuwar da wannan mummunan al’amari ya shafa, sannan yana ba su tabbacin samun tallafi daga gwamnatinsa.

Shugaban ƙasar ya kuma yi ƙira da a riƙa taka tsantsan da ɗaukar matakan kariya, domin kare afkuwar gobara da sauran bala’o’i a nan gaba.

Continue Reading

Gobara

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Published

on

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi da yammacin yau a wani sashe na matatar man Ɗangote da ke kusa da Lekki a Legas.

Jami’an agajin gaggawa sun ɗauki matakin shawo kan lamarin, kuma a cewar rahotannin farko, ba a samu raunuka ba.

Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano girman barnar da aka yi da kuma abin da ya haddasa faruwar lamarin.

Da take mayar da martani kan gobarar a cikin wata sanarwa da Ɗangote ya fitar, mai ɗauke da sa hannun Anthony Chiejina, ƙungiyar ta ce, “Mun yi gaggawar shawo kan wata ‘yar karamar gobara a masana’antar sarrafa iska (ETP), a yau Laraba 26 ga watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta kashe jarirai shida a Indiya

“Babu wani dalili na tashin hankali yayin da matatar ta ke aiki kuma babu wani rauni da aka samu ko lahani ga dukkan ma’aikatanmu da ke bakin aiki.”

Matatar dangote wani katafaren aiki ne da ake ginawa wanda ake hasashen zai iya tace ganga 650,000 a kowace rana.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like