Connect with us

Ƙasashen Waje

Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Published

on

Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya - Emine Erdogan

Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Uwargidan Erdogan a ranar Talata ta bayyana mummunan yanayin da yara ƙanana ke fuskanta a Gaza a jawabinta na Ranar Kare Iyali, tare da yin tir da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa. Ta buƙaci haɗin kan duniya don karewa da tallafawa masu rauni.

Ta ce akwai akalla yara 17,000 da ke watangaririya ba tare da iyalansu ba a Gaza kuma ba su da inda za su je.

“A yau, abin takaici ne cewa a sassa daban-daban na duniya, yara suna rayuwa a cikin munanan yanayi, suna fafitikar rayuwa, balle a ce suna da damar rayuwa cikin jin dadi ta iyalai,” in ji Erdogan.

Ta jadada tsananin al’amarin, inda ta yi nuni da cewa, ana kyautata zaton yara 4,000 suke maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-ginen da aka rusa ko kuma sun ɓata.

Erdogan ta ce yaran Falasdinawan da Isra’ila ta yi musu ta’asar da babu wani lamiri da zai goyi bayan hakan, an yi musu da tabon da ba zai warke ba.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Akalla Falasɗinawa 37,900 galibi mata da yara ne aka kashe yayin da 87,060 suka jikkata a Gaza tun lokacin da Tel Aviv ta kaddamar da farmaki a ranar 7 ga Oktoba, a cewar jami’an kiwon lafiya na yankin.

Fiye da watanni takwas da hare-haren Isra’ila, manyan yankunan Gaza sun zama kufai, a cikin yanayi na takunkuman hana shigar mata da abinci da ruwan sha da magunguna.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

Published

on

Wani jirgin ruwa ya kife da 'yan ci-rani a tekun Mauritania

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

‘Yan ci-rani kimanin 90 ne suka rasu a kan hanyarsu ta zuwa Turai a lokacin da jirgin ruwan da suke ciki ya kife a farkon makon nan a gabar tekun Mauritania, in ji kafar watsa labarai ta ƙasar wadda ta ambato jami’ai na bayani a ranar Alhamis.

Ana kuma ci gaba da neman da dama da suka bata.

“Jami’an tsaron teku na Mauritania sun gano gawawwakin mutane 89 da suka hau wani babban jirgin ruwan masunta da ya kife a ranar Litinin 1 ga Yuli a gabar tekun Atlantika,” kusan nisan kilomita huɗu daga gabar garin Ndiago a kudu maso-yammacin kasar, in ji kamfanin dillancin labarai na Mauritania a ranar Alhamis.

Jami’an tsaron iyakokin tekun sun kuma kuɓutar da wasu mutanen tara, ciki har da wata yarinya ‘yar shekara biyar, in ji kafar yaɗa labaran.

Kamfanin dillancin labaran ya rawaito cewa wadanda suka kuɓuta na cewa jirgin nasu ya taso ne daga iyakar Senegal da Gambia dauke da fasinja 170, wanda hakan ya sanya ake neman mutane 72 da suka ɓata.

Wani babban jami’in karamar hukuma a yankin da ya nemi a boye sunansa ya tabbatar wa AFP aukuwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Hanyar tekun Atlantika na da hatsari sosai saboda manyan igiyar ruwa, kuma ‘yan ci-rani na yin lodin da ya haura ka’ida a jiragen ruwa, a mafi yawan lokuta jiragen ba su da ingancin shiga teku, kuma ba sa ɗaukar isassen ruwan sha.

Amma hakan ya sake fitowa fili ne sakamakon yadda ake ƙara sanya idanu kan tekun Bahar Rum.

A shekarar 2023 adadin ‘yan ci-rani da suke zuwa tsibiran Canary na Sifaniya ya ninka a shekara guda, wanda ya kai mutane 39,910, kamar yadda gwamnatin Sifaniya ta bayyana.

Tsibiran Canary na Sifaniya na daura da iyakar tekun arewacin Afirka da nisan kilomita 100.

Amma jiragen ruwa da dama – mafi yawansu na katako – na kama hanya daga Maroko, Yammacin Sahara, Mauritania, Gambia da Senegal don zuwa tsibiran na Sifaniya.

Sama da ‘yan ci-rani 5,000 ne suka mutu a teku yayin ƙoƙarin tsallaka wa Sifaniya a watanni biyar na farkon wannan shekarar, kenan mutane 33 ne ke mutuwa kowacce rana, kamar yadda Caminando Fronteras, wata ƙungiyar bayar da agaji ta Sifaniya ta bayyana.

Wannan ne adadin rasa rayuka mafi yawa tun bayan da kungiyar ta fara tattara bayanai a 2007, kuma mafi yawa na mutuwa ne a hanyar tekun Atlantika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Jami’yyar adawa ta karɓe mulki a Birtaniya

Published

on

Jami’yyar adawa ta karɓe mulki a Birtaniya

Jami’yyar adawa ta karɓe mulki a Birtaniya

Jami’yyar adawa ta Labour ta kawo ƙarshen shekara 14 na mulkin Jam’iyyar Conservative a ƙasar Birtaniya.

Kazalika Labour ta ƙwace kujerar tsohuwar fira ministar Birtaniya Liz Truss da ke wakiltar mazabar Norfolk ta Kudu maso Yamma a Majalisar Dokokin ƙasar.

Jam’iyyar Labour ta kafa tarihin doke Conservative ne bayan zaɓen ranar 5 ga watan Yuli inda ta samu rinjayen kujeru a majalisar dokokin ƙasar.

A yayin da zaɓen ke ci gaba da kirga ƙuri’u, Fira Minista Rishi Sunak, ya amsa shan kayi.

Ya sanar da cewa, “na ɗauki laifin wannan faɗuwa da muka yi.”

Da wannan shan kaye, Rishi Sunak zai sauka daga kujerar Fira Ministan, wadda Shugaban Jam’iyyar Labour, Keir Starmer, zai ɗare domin kafa sabuwar gwamnati.

KU KUMA KARANTA: Za mu shiga zaɓen ƙananan hukumomi a Yobe — Jam’iyyun Adawa

Da yake jawabi, Starmer ya ce, “yau mun buɗe wani sabon babi a Birtaniya.”

Ya ci gaba da cewa, “nasarar zaɓe ba daga sama take faɗowa ba, sai da yaki da gwagwarmaya.

“Shi ya sa a wannan karo Jam’iyyar Labour ta kai ga narasa.”

Continue Reading

Ƙasashen Waje

An naɗa tsohon shugaban ‘yan daba Ministan Wasanni na Afirka ta Kudu

Published

on

An naɗa tsohon shugaban 'yan daba Ministan Wasanni na Afirka ta Kudu

An naɗa tsohon shugaban ‘yan daba Ministan Wasanni na Afirka ta Kudu

A wannan makon ne aka naɗa tsohon shugaban ƙungiyar ‘yan daba mai shekaru 50 a cikin majalisar ministocin ƙasar Afirka ta Kudu yayin da ƙasar ta kafa gwamnatin haɗin kan ƙasa (GNU) da Shugaba Cyril Ramaphosa ya ƙaddamar.

Hakan dai na zuwa ne bayan da jam’iyyar ANC mai rinjaye ta rasa rinjayen ‘yan majalisar dokokin ƙasar inda aka tilasta mata shiga ƙawance da jam’iyyun adawa.

An naɗa McKenzie – shugaban jam’iyyar Patriotic Alliance (PA) a matsayin Ministan Wasanni, Fasaha da Al’adu.

Kuma a ranar Laraba aka rantsar da shi tare da sauran takwarorinsa na majalisar ministocin, kuma ko a wajen sai da ya sanya mutane raha cikin barkwanci wanda ke nuni da irin laifin da ya aikata a baya.

“Lokaci na ƙarshe da wani alkali ya buƙaci na zauna, sai zaman ya zo da yanke min hukunci na tsawon shekara 10 a gidan yari,” ya faɗa cikin raha a lokacin da alkalin alkalan ƙasar Raymond Zondo ya buƙaci ya zauna don ya sanya hannu kan takardar rantsuwar zama minista.

“Wannan ya daɗe da wucewa)!” Alkalin Alkalan ya amsa da dariya tare da waɗanda suka halarci taron.

KU KUMA KARANTA: Yalon kati ya hana Slovenia hawa mataki na biyu a guruf ɗin gasar Euro 2024

Magoya bayan McKenzie sun ce labarin rayuwarsa daga zama shugaban ƙungiyar ‘yan daba a lokacin da yake da shekaru 16 zuwa zama minista a gwamnati, lamarin da ba a taɓa yin irinsa ba, wani ƙwarin gwiwa ne na shawo kan matsalolin rayuwa.

“Rayuwata ta ƙunshi shiga da fita gidan yari. Ba da daɗewa ba na zama wanda ake nema ruwa a jallo a sassa daban-daban na ’yan sanda. An kama ni ina da shekaru 21 a ƙarshe, ”in ji Ministan a cikin wasu jerin saƙonni da ya wallafa a shafin X.

“Na bayyana a kotu kuma an yanke min hukuncin ɗaurin shekaru 17 a gidan yarin Grootvlei.”

A lokacin, zuwa gidan yari tamkar alama ce ta girmamawa, in ji McKenzie. “Ba da daɗewa ba na yi shugabancin fursunonin gidan yarin gaba ɗaya kuma babu abin da zai faru a gidan yarin ba tare da na faɗa ba.”

Bayan an sake shi ya tsunduma cikin harkokin kasuwanci daban-daban – tun daga sayar da kifi, da gudanar da gidajen rawa da kuma saka hannun jari a harkar hakar ma’adinai.

Ya kuma kafa kamfanin buga littattafai da sayar da litattafai masu motsa rai daga abubuwan da suka faru a rayuwarsa.

Ya zama miloniya ta ƙiyasinsa. Amma sai da ya yi hatsarin mota kafin ya kai ga fara ganin sauyin rayuwa.

Ba da jimawa ba ya mayar da hankalinsa kan harkokin siyasa inda ya kafa jam’iyyarsa ta Patriotic Alliance a shekarar 2013 wacce ke da matsananciyar matsaya a kan harkokin shige da fice.

Ta lashe kashi biyu cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa a ƙasar a zaɓen na ranar 29 ga watan Mayu, tare da nuna ƙwazo a lardin Western Cape, inda ta samu kashi takwas cikin 100 na kuri’un. Ta lashe kujeru tara na Majalisar Dokoki ta Kasa.

Lokacin da Shugaba Ramaphosa ya fara zawarcin jam’iyyun da za a kafa gwamnatin hadin gwiwa, McKenzie ya fito fili ya bayyana sha’awarsa ga ma’aikatar harkokin cikin gida, mai kula da shige da fice. Sai dai ya ƙara da cewa zai kasance mai gaskiya a tattaunawar.

“Ba mu da isassun kujerun da za su sanya mu a matsayin da za mu shata layi,” in ji shi a cikin wani sakon X.

“Za mu saurari shawarar shugaban ƙasa kuma za mu mutunta ‘yancin da kundin tsarin mulki ya ba shi na yanke shawarar wanda yake so a majalisarsa.”

Majalisar ministocin Ramaphosa mai mambobi 32 tana da ƙarin mataimakan ministoci 43 kuma ta sha suka daga jama’a da cewaan debi mutane da yawa a lokacin da ake cikin halin taɓarɓarewar tattalin arziki. Duk da haka, McKenzie yana da kyakkyawan fata game da sakamakon gwamnatin haɗin gwiwar.

“Rayuwa ta koya mani cewa wani lokacin yana da kyau a yi fada daga ciki fiye da daga waje, hakan kuma ya koya min cewa a cikin tattaunawar ba za ku taba samun duk abin da kuke so ba.
Ina son Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, ban samu ba,” kamar yadda ya wallafa a shafin X bayan sanar da jerin sunayen ministocin.

McKenzie ya yi alkawarin bayar da dukkanin albashinsa na majalisa ga gidauniyar Joshlin Smith da ke kula da yaran da suka ɓace, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na cikin gida suka ruwaito.

“Kashi 100 na albashina zan bai wa gidauniyar Joshlin Smith mai kula da harkokin yaran da suka ɓace na tsawon zamana a majalisar, kashi 100 na albashina ba 80% ko 50% ba… Saboda ban zo nan don kuɗi ba. Na zo ne domin in sauya rayuwar mutanenmu,” in ji shi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like