Connect with us

Nishadi

Cece kuce akan yawan taliyar leda

Published

on

Rahotanni daga majiya me qarfi sun zo mana cewa an rage yawan taliyar Leda.

Wani matsahi ya gaya ma wakilan mu cewa, an zare guda hudu a ciki, sannan an rage mata kauri, kana an ƙarawa ledar iska??..Ba a tsaya anan ba, seda aka ƙara mata handaret naira?.

Mun sami labari cewa an zare tsinke 34 na taliyar leda, a gaskiya ba haka ba ne, domin bincken ya tabbatar mana da cewa tsinke sha takwas ake zarewa daga kamfani, inda masu shaguna kan zari tsinke hudu, jimillar abinda aka zare ya zama tsinke 24 kenan.

Domin kawo qarshen wannan cece kuce, muna bawa me karatu shawara ya siyo taliyar leda ya ƙirga da kansa, domin sanin taƙamaimai guda nawa ne a ciki?. Masu iya magana kance, ‘yi da kai, yafi saqo’.

Mudai daga Neptune, fatanmu, Allah Ya Kawo mana sauqin tsadar kayan abinci. Amin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

An haramta shirya fina-finan da ke nuna ƴan daudu da ƴan daba a Kano

Published

on

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta haramta shirya fina-finai da ke nuna faɗan daba da harkar Daudu a Kano.

Shugaban hukumar Abba El-Mustapha ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da hukumar ta tace fina-finan ta fitar a ranar Laraba.

Hukumar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne bayan ta tattauna da ma’aikatan hukumar da wasu daga cikin wakilan yan masana’antar shirya fina-finan ta kannywood waɗanda suka haɗa da ƙungiyoyin MOPPAN, Arewa Film Makers da daraktoci da kuma furodusoshi.

Abba ya ƙara da cewa doka ce ta bai wa hukumar damar dakatarwa ko hana duk wani film da take ganin ya ci karo da tarbiya tare da al’adar al’ummar da ke jihar.

KU KUMA KARANTA: Kannywood ta ba wa Hisbah tabbacin goyon baya a Kano

“Tuni lokaci ya shige da za’a saka ido irin wannan gurbatattun fina-finai su ci gaba da yaɗuwa a cikin al’umma,” in ji shi.

Ko a kwanakin baya sai da hukumar ta ɗauki matakin rufe gidajen gala a jihar inda ta ce har sai bayan azumin watan Ramadana.

Continue Reading

Nishadi

Ali Nuhu ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan kwaikwayo na Nollywood ‘Europe Golden Awards’

Published

on

Fitaccen jarumin nan na Najeriya Ali Nuhu wanda fitaccen jarumin fina-finan Kannywood ne, ya samu kyautar gwarzon ɗan wasa a ‘Nollywood Europe Golden Awards’.

Ali Nuhu na ɗaya daga cikin fitattun jaruman fina-finan Nollywood da na Kannywood wanda ya ɗauki hankulan mutane da dama a Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

Lambar Yabo

Ba wai mutanen Najeriya kawai ne suke son wasan kwaikwayonsa ba amma mutanen Turai da sauran ƙasashen waje.

Ali Nuhu yana da shekaru 49 ya samu nasarori da dama.

An san shi da tawali’u da himma a cikin aikinsa.

KU KUMA KARANTA: Rahama Sadau da Ali Nuhu sun jagoranci Fim ɗin Hausa na farko a Netflix don bunƙasa al’adun Arewa

Ya fito a fina-finai da dama da suka haɗa da garin Shanty da sauran fina-finai da dama waɗanda suka sa ya shahara sosai.

Mutane suna ƙaunarsa sosai kuma suna farin cikin ganin ya yi fice. Mutanen da suka ga rubutun nasa mintuna kaɗan da suka gabata suna taya murna saboda kasancewarsa gwarzon jarumin Nollywood a Turai Golden Awards a bana.

Continue Reading

Nishadi

Yadda Uba ya auri bazawara don nema wa ɗansa auren ‘yarta

Published

on

Wata bazawara ta kasance tana riƙon wata kyakkyawar budurwa. Duk wanda ya zo neman aurenta sai Bazawarar ta ce, ita ba za ta ba da aurenta ba sai an biya kuɗin aure da ɗawainiyarsa naira Miliyan 20, babu ragin ko sisi. Da yawan samari suka haƙura da aurenta.

READ ALSO: Almubazzaraci ya sa an kori ’yan sandan Imo bakwai, an gurfanar da su gaban kuliya

Wani saurayi, ya ga budurwar nan yana sonta, ita kuma ta gaya masa ƙa’idar aurenta. Saurayi ya je gida ya faɗawa Babansa tsarin auren budurwar da yake so. Saurayi ya ce, yana da Naira Miliyan 15 ta ribar kamfaninsa da ya samu.

Babansa ya ce, kawo miliyan 15 ɗin, saurayi ya kawo. Babansa ya ɗauke shi suka tafi gidan Bazawarar nan.

Babansa ya ce, zan yi magana amma kar ki katse ni sai na je ƙarshe. Bazawara ta ce, to.

Baban Saurayi ya ce, ga miliyan 5 kuɗin auren ‘yar da kike riƙo. Za ta yi magana ya ce, ta yi shiru. Ga kuma Naira miliyan 5, ni mahaifin wannan yaro na ganki ina sonki, zan aureki.

Take Bazawara ta ce masha Allah, Alhamdulillah! komai ya yi daidai, Allah ya bamu zaman lafiya. Sai a ɗaura kawai.

Mutane suka ce, ke da kike neman miliyan 20, ta yaya kika ƙare a miliyan 10? Sai ta ce Allah sarki, sayan jimla, ai ba daidai yake da sayan ɗaiɗai ba.

Shi kuma Saurayi ya yiwa babansa godiya ya ce, har canjin 5m na samu, sai a bani na ƙarasa ɗawainiyar biki. Baban ya ce, Kai ba ka da hankali ne, ba ka fahimtar lissafi, wannan miliyan 5 ɗin da ta rage mahaifiyarka za a bawa na dannar ƙirji.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like