Connect with us

Ƙasashen Waje

Bankin duniya ta baiwa Togo kyautar dala miliyan 200 don magance matsalar lantarki

Published

on

Bankin duniya ta baiwa Togo kyautar dala miliyan 200 don magance matsalar lantarki

Bankin duniya ta baiwa Togo kyautar dala miliyan 200 don magance matsalar lantarki

Bankin Duniya ta amince da bai wa Togo dala miliyan 200 don magance matsalar samar da wutar lantarkin da kasar ke fama da ita na tsawon watanni.

A dai-dai lokacin da za a fara babban zaɓen ƙasar, a ƴan watannin nan, Togo na fuskantar matsananciyar matsalar rashin wutar lantarki, lamarin da ya haddasa tsadar rayuwa a ƙasar.

Ministan tattalin arziki da kuɗin Togo, Sani Yaya, ya bayyana farin cikinsu game da samun wannan tallafi, sannan ya ce kudin zai agaza wurin gina manyan layin wuta wanda hakan zai taimaka wa ƴan ƙasar da ke rayuwa a ƙauyuka wajen samun wutar cikin sauƙi.

Ministan ya ƙara da cewa wannan tallafi zai sa sama da mutane miliyan ɗaya da rabi su samu wutar lantarki mara katsewa.

KU KUMA KARANTA: Bankin Duniya na gargaɗi kan ‘matsananciyar yunwa’ a Gaza

Matsalar ƙarancin wutar da aka fuskanta na zuwa ne bayan Najeriya wacce ita ce ke bai wa Togon da Nijar da kuma Benin lantarki ta bayyana takaita adadin wutar da za ta dinga ba su a ranar 1 ga watan Mayun shekarar nan.

Hukumar da ke kula da wutar lantarkin ta ce Najeriya wacce ita ce ta fi ba su wutar na bin su bashin miliyoyin daloli na lantarkin da suka sha kuma suka kasa biya.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Ƙasashen Waje

Mutum 129 sun mutu, sama da 120 suka jikkata sakamakon ambaliyar ruwa

Published

on

Mutum 129 sun mutu, sama da 120 suka jikkata sakamakon ambaliyar ruwa

Mutum 129 sun mutu, sama da 120 suka jikkata sakamakon ambaliyar ruwa

Mummunan iftila’in ambaliyar ruwa a Nijar ya yi sanadin mutuwar mutane da dama yayin da wasu kuma suka jikkata tun da aka shiga lokacin daminar bana a ƙasar.

Hukumar shirye-shirye da gargadi da kuma takaita aukuwar bala’o’i tare da kare al’umma (DPA/GC) a Nijar, ta ce ya zuwa 12 ga watan Augusta, 2024 iftila’in ya yi sanadin mutuwar mutum 129, yayin da wasu mutum 126 kuma suka jikkata.

Rahotanni sun yi nuni da cewa, al’ummomi 28,000 ne iftila’in ya shafa, yayin da gidaje 23,619 suka rushe sannan an yi asarar dabbobi 16,000, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta Actuniger ta rawaito.

Yawan adadin da ɓarnar ta haifar ya ƙaru sosai idan aka kwatanta da adadin da ministar ayyukan jinƙai da takaita aukuwar bala’o’i a Nijar, Madam Aissa Laouan Wandarama ta bayyana ya zuwa ranar 7 ga watan Agusta.

KU KUMA KARANTA: Ambaliyar ruwa a Jigawa tayi sanadiyar mutuwar mutane 16 tare lalata gidaje da dama

Rahoton bayanan da aka tattaro a lokacin ya yi nuni da cewa, mutum 94 ne suka mutu, daga ciki an rasa 44 daga kai-tsaye sakamakon ambaliyar ruwan, yayin da 50 kuma suka mutu a ruftawar gidaje.

Kazalika adadin mutanen da lamarin ya shafa a lokacin ya kai 137,156, inda gidaje 14,045 suka rushe sai kuma ɓukkoki 502 sun lalace.

An kuma yi asasar dabbobi 15,470, daga ciki akwai ƙananan dabbobin gida 13,981 da kuma manya 297.

Sannan ambaliyar ta shafe kadada 2,763 na gonakin noma a Nijar, inda aka yi asarar ton 17,495 na kayan amfanin gona tare da jikkata mutane 93.

Rahotannin baya-bayan nan dai sun nuna yadda iftila’in ya haifar da mummunar barna a kusan dukka faɗin yankunan Nijar, inda ta shafi ababen more rayuwa tare da katse hanyoyin tafiye-tafiye a ƙasar.

Ƙididdigar hasashen yanayi ta yi nuni da cewa akwai yiwuwar iftila’in ambaliyar ruwa a shekarar 2024 a yankunan Yammaci da tsakiyar Afirka ya zarce na shekarun baya.

Ta kuma ce hakan zai ta’azzara yanayin da al’ummomi ke ciki matuƙar ba a ɗauki matakan da suka kamata ba bisa ga tsarin kariya da muhimman matakan takaita tasirin sauyin yanayi da hukumomi suka bayar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta bai wa Falasɗinawan Gaza umarnin barin gidajensu – MƊD

Published

on

Isra'ila ta bai wa Falasɗinawan Gaza umarnin barin gidajensu - MƊD

Isra’ila ta bai wa Falasɗinawan Gaza umarnin barin gidajensu – MƊD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana girman mamayar da sojojin Isra’ila suke yi wa yankin Gaza, tana mai cewa an kori kusan kashi 84 daga yankin.

Da yake bayani kan alƙaluman da Ofishin Babban Mai Kula da Harkokin Jinƙai na Majalisar (OCHA) ya tattara, mataimakin kakakin ofishin Farhan Haq ya shaida wa manema labarai cewa “luguden wuta da kuma kutsen da Isra’ila take yi a Gaza na ci gaba da kashewa da jikkatawa tare da korar Falasɗinawa daga matsugunansu, da kuma rusa gidajensu da sauran gine-gine da suka dogara a kansu.”

Ya ce, “Sau biyu sojoji suna bayar da umarni ga mutane su fita daga Khan Younis a ƙarshen mako, zuwa yankunan da a baya galibi aka umarci mutane su fice daga cikinsu.”

KU KUMA KARANTA: Dubban Falasɗinawa sun tsere daga wani yanki a tsakiyar Gaza

Wannan lamari ya shafi yankuna 23 da wurare 14 da ke samar da ruwa da tsaftar jama’a da kuma makarantu huɗu.

“Jimilla, sojojin Isra’ila sun kori mutane daga wurin da ya kai girman murabba’in kilomita 305, wato kusan kashi 84 na yankin Zirin Gaza,” in ji shi.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

DR Congo da Zambia sun fara tattaunawa game da rufe kan iyaka

Published

on

DR Congo da Zambia sun fara tattaunawa game da rufe kan iyaka

DR Congo da Zambia sun fara tattaunawa game da rufe kan iyaka

Jamhuriyar Dimukuraɗiyyar Congo ta ce ta fara tattaunawa da Zambia kwana guda bayan da maƙociyarta ta kudancin Afirka ta rufe iyakarsu.

Matakin ya toshe babbar hanyar da Congo ke amfani da ita don fitar da Copper zuwa ƙasashen waje, a matsayinta na ƙasa ta biyu a duniya a yawan fitar da ƙarfen Copper.

A ranar asabar, ministan kasuwanci na Zambia, Chipoka Mulenga ya sanar da rufe iyakar na wani ɗan lokaci, bayan Congo ta saka haramcin amfani da lemon zaƙi da barasa da aka shigo da ita, inda ya haifar da zanga-zangar direbobin dakon kaya a garin Kasumbalesa da ke iyakar Zambia.

KU KUMA KARANTA: Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

“An fara tattaunawa tsakanin gwamnatocin Congo da Zambia tun ranar Lahadin nan, don hanzarta sake buɗe ƙofar iyakar tasu,” in ji wata sanarwa da Ma’aikatar Kasuwanci ta Congo ta fitar a ranar Lahadi.

“A awannin da suka biyo baya, ɓangarorin biyu za su haɗu a Lubumbashi da ke Haut-Katanga, don nemo mafita ta ƙarshe game da kasuwancin.”

Ministan Kasuwanci na Congo, Julien Paluku Kahongya, ya fitar da sanarwa a ranar Lahadi, inda yake cewa ma’aikatarsa ta samu sanarwa a hukumance game da taƙaddamar kasuwanci daga Zambia kafin ta sanar da rufe iyakar.

A sanarwar, ya yi dogon bayani game da yarjejeniyar kasuwancin ƙasashen biyu da kuma hanyoyin magance duk wata taƙaddama da ta taso.

“Ya zuwa yanzu babu wata taƙaddama da aka gabatar wa ma’aikatar a rubuce, ko ta hanyar diflomasiyya,” in ji shi. “Ma’aikatar ta shirya duba duk wata buƙata da Zambia ta kawo, matuƙar tana ƙunshe cikin yarjejeniyar, wadda ta hana ramuwar gayya.”

Congo ce ƙasa ta biyu a duniya a fannin samar da ƙarfen Copper, kuma ta zo ta 3 a 2023 wajen fitar da shi, bayan ta fitar da tan miliyan 2.84.

Zambia hanya ce mai muhimmanci ga Congo, wajen fitar da Copper, inda ake bi ta garin Kasumbalesa a shiga Zambia.

Continue Reading

You May Like