Connect with us

Labarai

APC ta ceto Najeriya daga wargajewa, Tunibu zai ɗora ya magance matsalar tsaro – Shinkafi

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Mahmud Aliyu Shinkafi, ya bayyana cewa nan ba da daɗewa ba Najeriya za ta samu zaman lafiya da kwanciyar hankali kamar yadda ta kasance kafin bullar kungiyoyin boko haram da ‘yan fashi da kuma kungiyar IPOB.

Shinkafi, wanda ya bayar da wannan tabbacin a ranar Lahadi, a lokacin da yake ƙaddamar da yakin neman zaben Sanata Sahabi Ya’u Ƙaura a karkashin jam’iyyar APC mai mulki, ya ce gwamnatin APC mai ci ta ceto ƙasar nan daga wargajewa.

Ya kara da cewa, Nijeriya a matsayin ta na kasa me ‘yan ci na shirin rugujewa saboda saurin karuwar manyan masu aikata laifuka ke yi, musamman a arewa maso gabashin ƙasar inda aka kashe dubban rayukan da ba su ji ba ba su gani ba.

KU KUMA KARANTA:Cikin Hotuna: Yadda aka yi jana’izar ɗan majalissar da ya rasu a taron Tinubu a Jos

“Abin da ’yan kasar mu suka kasa fahimtar dalilin da ya sa matsalolin rayuwa a ƙarkashin wannan gwamnati shi ne, abin da ya fi muhimmanci shi ne a yi la’akari da yaƙi, da ƙalubalen tsaro da ke addabar kasar wanda aka fara tun gwamnatin da ta gabata.

“Babu wani ci gaba mai ma’ana da za a samu ba tare da zaman lafiya ba, don haka dole ne gwamnatin Buhari ta taka muhimmiyar rawa wajen ganin Najeriya ta dore, kafin ta gudanar da ayyukan da ke kunshe cikin tsarin,” in ji Shinkafi.

Shinkafi ya ci gaba da cewa, yaki da masu aikata laifuffuka wanda ba a san su waye ba, yana da dabaru daban-daban, lamarin da ake kyautata zaton ya dauki wannan gwamnati kusan shekaru takwas, har zuwa kwanan nan da jami’an tsaro suka samu nasarar yaki a yankin arewa maso gabas, yayin da a halin yanzu suke yaƙin a yankin arewa maso yamma na yaƙi da ‘yan fashi.

“Zuwar Ahmed Bola Tinubu a matsayin shugaban kasa na gaba, idan aka zaɓe shi, zai karɓa daga wannan gwamnati, domin zai karfafa nasarar da aka samu a kan masu aikata laifuka, kuma duk abubuwan da ake sa ran ‘yan ƙasa su samu, za su biyo baya”, Shinkafi ya tabbatar.

Da yake jawabi, Sanata Sahabi Ya’u, ya yi kira ga dukkan waɗanda suka cancanci kada kuri’a a fadin mazabarsa ta Sanata, da suka hada da kananan hukumomin Kaura Namoda, Shinkafi, Zurmi da Birnin Magaji, da su yi amfani da kuri’unsu domin ci gaba da samun ci gaba a shiyyar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Bai kamata a zargi APC ba, don ta gaji matsalar tsaro- Aminu Jaji | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like