Soyayyar shekaru tara ta ƙare a bala’i, yayin da budurwa ta ƙona saurayinta a gidansa, ta kuma kashe kanta

0
454

Daga Fatima MONJA, Abuja

Labarin Masoyan biyu, Boluwatife Bamidele, da Ifeolowa, labarin soyayya ne ta yau da kullum wanda suke sa ran yin aure da tara zuri’ah.
Soyayyar shekaru tara ta ƙare a bala’i inda masoyan suka mutu gabaki ɗaya a dalilin cin amana.

Wadannan matasan masoyan sun yi baiko ranar 4 ha watan Oktoba 2021, dan tabbatar wa juna da duniya dagaske suke, kafin Boluwatife ya tafi ƙasar Kairo binkice kan kore makiyaya. Ya dawo ƙasar nan a farkon wannan wata dan yayi wa masoyiyar tashi Ifeolowa, bazatan kyauta ta zagayowar ranar haihuwarta. Dawowar da akayi domin farinciki tayi sanadin mutuwar Masoyan duka biyu.

A ranar Lahadi 17 ga watan Yuli ne Ifeolowa ta cilla wuta a gidansu dake Koka kusa da Osogbo, bayan ta gano masoyin nata na neman wata daban wanda har sun haihu da ita, bayan ita bata samu haihuwar ba.

Matashiyar buduwar ta gudu bayan aika-aikar da tayi, baa sameta ba sai ranar da aka kai ta Babban asibiti a dake Oshogbo a mace, inji lauyan ta.

Gabriel Adejare, daya kasance maƙoci ya ce “yaga Ifeolowa lokacin yana dawowa daga aiki tana tafiya ba takalma kuma cikin kayan ƙasan tufafi. Lokacin da yayi kusa da gidan su sai ya fara ganin hayaƙi, sai yayi kururuwa dan a kawo ɗauki ga Boluwatife, bayan Faith ƙanwar shi ta sanar musu yayanta cikin gidan.”

“Mun fasa tagogi 4 Kafin muka samu daman shiga mu fito da shi, muka kai shi asibiti, daganan aka tura mu asibitin koyarwa dake Ibadan, jihar Oyo.”

Bode ƙani, kuma lawyan Boluwatife ya sanar da folis da su nemo inda Ifeolowa take, domin be yadda da labarin kashe kanta da tayi ba. Yana ganin tayi hakan da gangan ne, don gudun tuhuma.

Amma kuma a safiyar jumma’a aka samu gawarta a ɗakin ajiye gawa tare da taimakon lauyanta.

Duk da Bode ya tabbatar da gawar ta Ifeolowa ce, babu wanda yasan sanadin mutuwarta.

An tabbatar da Ife ta canza muhalli zuwa Ilesa sannan ta kira lauyan yazo ya dauke ta a ranar jumma’ah.

Tasha guba ta ne kafin isowar lauyan nata, ta dai samu ta bashi wasu takaddu da ta rubuta kafin ta fita daga haiyacin ta.

Daga cikin abinda ta rubuta shine, “Abokai na na kwarai da suke sona kuma suke sauraro na Mummy Fife, DJ whizz, Mummy Laurel, Mhiz Ammie, Adeoluwafemi, Dimeji, Odunola, Tiara. Ina son ku duka na aiko muku wannan ne domin nuna godiya da soyayyar ku gareni.”

“Omobaba, VP, Alahusa Fourty, My baby, Mummy Love… ku tabbatar da tambarin Teembam ya ɗore, tare da nawa. Kada ku manta da IFETIFE.”

“Ban kashe abokin ku ba, dan dukan ku kunsan ina tsananin son shi, sannan na cigaba da son shi har yanzu da nake gaɓar mutuwa. Kuyi bincike da kyau, musamman Omobaba da Fourty. Na dogara daku, kuma nasan Boluwatife zaiji dadin hakan.

Ɗan sanda mai magana da yawun hukumar, ya tabbatar da mutuwar Boluwatife, ta sanadin wuta da budurwar sa ta cinna mai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here