Connect with us

Ƙasashen Waje

Ana zaɓen shugaban ƙasa a Chadi

Published

on

A yau Litinin ne al’ummar ƙasar Chadi suka fara kaɗa ƙuri’a a zaɓen Shugaban Ƙasa, a karo na farko cikin shekara uku bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi.

An buɗe rumfunan zaɓen ne da misalin ƙarfe 7 na safe agogon ƙasar, inda za a rufe su da ƙarfe biyar na yamma, kuma mutum miliyan 8.5 ne suka yi rajistar zaɓen.

Sai dai tun a jiya Lahadi ne sojoji suka kaɗa nasu ƙuri’un.

Ana sa ran sakamakon farko-farko zai samu zuwa ranar 21 ga watan Mayu, yayin da illaharin sakamakon zai samu ranar 5 ga watan Yuni.

Idan har babu ɗan takarar da ya yi nasara da samun kashi 50 cikin 100 na zaɓen, to za a je zagaye na biyu ranar 22 ga watan Yuni.

Masu sharhi sun ce shugaba mai ci Mahamat Idriss Deby, wanda ya karɓi mulki bayan da ƴan tawaye suka kashe mahaifinsa Idriss Deby da ya shafe tsawon shekaru yana mulki, a watan Afrilun 2021, ga alama shi ne zai yi nasara a zaɓen, duk da cewa babban abokin karawarsa yana samun magoya baya fiye da yadda aka yi tsammani a yayin yaƙin neman zaɓe.

KU KUMA KARANTA: Amurka za ta janye dakarunta daga Chadi

A cikin alkawuransa na yaƙin neman zaɓe, Deby ya ce zai ƙarfafa tsaro da ƙarfafa doka da kuma ƙara samar da wutar lantarki.

Zaɓen dai ya zo daidai da janyewar sojojin Amurka na wucin gadi daga kasar Chadi, wani muhimmin ƙawancen Ƙasashen Yammacin Duniya a yankin yammacin Afirka da kuma tsakiyar Afirka da Rasha ke neman samun ƙarfin faɗa a ji a wajen.

Tun lokacin da ya maye gurbin mahaifinsa a kan mulkin kasar ta yankin Afirka ta Tsakiya, Deby ya ci gaba da kasancewa ƙut-da-ƙut da ƙasar da ta yi musu mulkin mallaka wato Faransa.

Yayin da sauran kasashen yankin Sahel da ke karkashin mulkin soja da suka hada da Mali da Burkina Faso da Nijar suka shaida wa Faramasa da sauran Ƙasashen Yammacin Duniya da su janye daga gare su, inda suka koma wa neman goyon bayan Rasha, ita kuwa Chadi har yanzu akwai sojojin Faransa masu yawa a cikinta.

Sai dai Amurka ta sanar da janye akalla wasu sojojin na wucin gadi a watan da ya gabata, inda ta ce za ta ci gaba da duba ayyukan tsaro bayan zaben.

Zaɓen na ranar Litinin ya jawo an samu ɓaraka a tsakanin Deby da firaministansa Succes Masra, wanda a baya abokin hamayyar siyasa ne da ya yi gudun hijira a shekarar 2022 amma bayan shekara guda aka ba shi damar komawa ƙasar.

Haka kuma akwai tsohon Firaminista Albert Pahimi Padacke da wasu ‘yan takara bakwai da ke fafatawa a zaɓen.

Shi kuwae Yaya Dillo, ɗan siyasar adawa da aka yi tsammanin zai fafata da Deby duk da cewa sun fito daga ƙabila ɗaya, an harbe shi har lahira a babban birnin N’Djamena a ranar 28 ga watan Fabrairu, ranar da aka saka ranar zaɓen.

Padacke ya zargi Masra da hada kai da Deby. Amma shi ma Masra yana da tasa jama’ar da yawa da suka halarci gangaminsa.

Wasu ‘yan adawa da kungiyoyin farar hula sun yi kira da a ƙaurace wa zaɓen, saboda fargabar yiwuwar za a yi maguɗin.

Hakan ya haifar da fargabar yiwuwar tashin hankali. Baniara Yoyana, wani tsohon minista kuma alkali ya ce “Wannan zaben shugaban kasa yana da matukar muhimmanci ga kasar nan, domin al’ummar kasar baki daya na fatan ya kawo sauyi. Dole ne a yi zaɓen cikin gaskiya da sahihanci don kauce wa duk wani hadarin da zai iya haifar da rikici.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Published

on

Dakta Mas'ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Waye Dakta Mas’ud Pezeshkian sabon shugaban ƙasar Iran na 9 cikin shekaru 45 ataƙaice?

An haife shi a ranar 29 ga Satumba, 1954, a Mahabad, a yammacin lardin Azarbaijan, Dakta Mas’ud Pezeshkian ya wakilci birnin Tabriz da ke arewa maso yammacin kasar a majalisar dokokin Iran ta 12.

Ya riƙe muhimmin muƙamai a majalisar a Hukumomi daban-daban matakin gwamnatin tarayya, kuma ya zama ministan lafiya a lokacin mulkin Shugaba Mohammad Khatami (2001-2005). Duk da cewa an tsige shi bayan wasu lokuta saboda gaza cimma wasu ayyuka da kawo sauyi.

An zaɓe Pezeshkian a majalissar 8th, 9th, 10th, and 11th. A tsakanin shekarar 2016 zuwa 2020, ya kuma rike mukamin mataimakin shugaban majalisar na farko. A baya dai ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2013 da 2021 amma ya kasa samun nasara a lokuta biyun.

KU KUMA KARANTA: An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Dr. Mas’ud Pezeshkian likitan zuciya ne kuma me koyarwa, ya yi aiki a matsayin shugabar Jami’ar Tabriz ta Kimiyyar kiwon lafiya, kuma a halin yanzu memba ne na ma’aikatan ilimi a wannan babbar jami’a a arewacin Iran.

Bayan da ya samu amincewa daga babbar hukumar da ke sa ido kan zabukan kasar na ya tsaya takara a zaben na ranar 28 ga watan Yuni a watan da ya gabata. Ya gabatar da tsare-tsarensa, inda ya jaddada muhimmancin damka ayyuka ga kwararru kuma masu ilimi a gwamnatinsa.

Haka nan kuma ya bayyana Javad Zarif, tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran a matsayin zabinsa na shugabancin ma’aikatar harkokin wajen kasar, yayin da ya sha alwashin aiwatar da umarnin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Pezeshkian a hukumance ya shiga takarar neman kujerar shugaban kasar a ranar 1 ga watan Yuni, rana ta uku ta rajista, a ma’aikatar harkokin cikin gida da ke Tehran, tare da rakiyar gungun magoya bayanta.

A muhawarar zagaye na biyu na zaben shugaban kasa, Pezeshkian ya bayyana mahimmancin kiyayewa da cika alkawura a matsayin wani muhimmin al’amari na kiyaye kyawawan halaye.

Ya jaddada muhimmancin nuna girmamawa ga daidaikun mutane, tabbatar da jin muryoyinsu, da bayar da shawarwari kan ayyuka bisa ka’idojin adalci da adalci.

Tsohon ministan lafiya ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da amana ke takawa wajen ciyar da al’umma gaba, tare da jaddada cewa gaskiya na da matukar muhimmanci wajen samar da amana a tsakanin al’umma.

Pezeshkian ya jaddada muhimmancin ba da fifiko kan dangantaka da kasashen dake makwabtaka da ita, da fadada huldar dake tsakanin kasashen duniya don bunkasa ci gaban kasar.

A lokuta da dama, ya nanata kudurinsa na mutunta tsarin dokokin Jamhuriyar Musulunci da kuma manufofin da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamene ya bayyana.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Published

on

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra'ila

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyar Hezbollah mai da ke Lebanon ta ƙaddamar da hare-haren rokoki fiye da 200 da jirage marasa matuƙa zuwa arewacin Isra’ila, a wani martani na kisan ɗaya daga cikin manyan kwamandojinta.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce an kashe sojanta da dama a hare-haren, na Hezbollah.

Sojojin na Isra’ila sun kuma ce sun mayar da martani kan mayaƙan ƙungiyar da sansanoninta da ke kudancin Lebanon.

Kafofin yaɗa labaran Lebanon sun ce mutum guda ya mutu a wani harin jirgi maras matuƙi da Isra’ila ta kai garin Houla.

Hare-haren na baya-bayan nan, sun kasance mafiya muni cikin watanni tara tsakanin kan iyakokin ƙasashen biyu.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

An kashe ɗaya daga cikin kwamandojin Hezbollaha wani hari ta sama da Isra’ila ta kai birnin Tyre na ƙasar Lebanon.

Mohammed Nimah Nasser, ya kasance ɗaya daga cikin manyan jagororin ƙungiyar, kafin kisan nasa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

Published

on

Wani jirgin ruwa ya kife da 'yan ci-rani a tekun Mauritania

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

‘Yan ci-rani kimanin 90 ne suka rasu a kan hanyarsu ta zuwa Turai a lokacin da jirgin ruwan da suke ciki ya kife a farkon makon nan a gabar tekun Mauritania, in ji kafar watsa labarai ta ƙasar wadda ta ambato jami’ai na bayani a ranar Alhamis.

Ana kuma ci gaba da neman da dama da suka bata.

“Jami’an tsaron teku na Mauritania sun gano gawawwakin mutane 89 da suka hau wani babban jirgin ruwan masunta da ya kife a ranar Litinin 1 ga Yuli a gabar tekun Atlantika,” kusan nisan kilomita huɗu daga gabar garin Ndiago a kudu maso-yammacin kasar, in ji kamfanin dillancin labarai na Mauritania a ranar Alhamis.

Jami’an tsaron iyakokin tekun sun kuma kuɓutar da wasu mutanen tara, ciki har da wata yarinya ‘yar shekara biyar, in ji kafar yaɗa labaran.

Kamfanin dillancin labaran ya rawaito cewa wadanda suka kuɓuta na cewa jirgin nasu ya taso ne daga iyakar Senegal da Gambia dauke da fasinja 170, wanda hakan ya sanya ake neman mutane 72 da suka ɓata.

Wani babban jami’in karamar hukuma a yankin da ya nemi a boye sunansa ya tabbatar wa AFP aukuwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Hanyar tekun Atlantika na da hatsari sosai saboda manyan igiyar ruwa, kuma ‘yan ci-rani na yin lodin da ya haura ka’ida a jiragen ruwa, a mafi yawan lokuta jiragen ba su da ingancin shiga teku, kuma ba sa ɗaukar isassen ruwan sha.

Amma hakan ya sake fitowa fili ne sakamakon yadda ake ƙara sanya idanu kan tekun Bahar Rum.

A shekarar 2023 adadin ‘yan ci-rani da suke zuwa tsibiran Canary na Sifaniya ya ninka a shekara guda, wanda ya kai mutane 39,910, kamar yadda gwamnatin Sifaniya ta bayyana.

Tsibiran Canary na Sifaniya na daura da iyakar tekun arewacin Afirka da nisan kilomita 100.

Amma jiragen ruwa da dama – mafi yawansu na katako – na kama hanya daga Maroko, Yammacin Sahara, Mauritania, Gambia da Senegal don zuwa tsibiran na Sifaniya.

Sama da ‘yan ci-rani 5,000 ne suka mutu a teku yayin ƙoƙarin tsallaka wa Sifaniya a watanni biyar na farkon wannan shekarar, kenan mutane 33 ne ke mutuwa kowacce rana, kamar yadda Caminando Fronteras, wata ƙungiyar bayar da agaji ta Sifaniya ta bayyana.

Wannan ne adadin rasa rayuka mafi yawa tun bayan da kungiyar ta fara tattara bayanai a 2007, kuma mafi yawa na mutuwa ne a hanyar tekun Atlantika.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like