Connect with us

Zaɓen 2023

An tsaurara tsaro a wajen ci gaba da tattara sakamakon zaɓe a Adamawa

Published

on

An tsaurara tsaro a lokacin da jami’an hukumar zaɓe mai zaman kanta na ƙasa (INEC) suka sake taro a cibiyar tattara sakamakon zaɓe a jihar Adamawa

Jami’an tsaro sun isa cibiyar tattara sakamakon zaɓen jihar da ke Yola, babban birnin jihar Adamawa yayin da jami’an hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ke ci gaba da zama.

‘News Point’ Nigeria ta ruwaito cewa, an ga sakataren hukumar zaɓe ta INEC a jihar, Adamu Gujungu, wanda aka ba da umarnin ya maye gurbin kwamishinan zaɓe Hudu Yunusa Ari a wurin tattara sakamakon zaɓen.

KU KUMA KARANTA: Ta maka INEC da PDP a kotu kan zargin ayyana ta a matsayin zaɓaɓɓiyar gwamnan Adamawa – Binani

Ana sa ran kwamishinan INEC na ƙasa kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a, Festus Okoye a wurin tattara sakamakon zaɓen.

A ranar Lahadi ne INEC ta dakatar da tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar Adamawa da aka gudanar a ranar Asabar bayan Ari ya bayyana Aisha Binani Ɗahiru na jam’iyyar APC a matsayin wacce ta lashe zaɓen tsakaninta da gwamna Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP.

Nan take INEC ta gayyaci Ari zuwa Abuja tare da ayyana sanarwar sa a matsayin shela marar inganci da kuma ƙwace ikon jami’an tattara bayanai da na dawo da su.

Alƙalin zaɓen ya kuma ce zai rubutawa Sufeto Janar na ‘yan sanda, Usman Baba domin ya binciki Ari. Kafin a dakatar da aikin tattara sakamakon a daren Asabar, an sanar da sakamakon ƙananan hukumomi 10 – kuma Binani tana bin Fintiri.

Da misalin ƙarfe 11 na safiyar Lahadi ne ake sa ran fara tattara sakamakon sauran ƙananan hukumomi 10 da suka rage, kuma Mele Lamido, jami’in zaɓen gwamnan Adamawa, bai halarci ba lokacin da Ari ya bayyana Binani a matsayin wanda ta lashe zaɓen.

Kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada, Lamiɗo ne jami’in da ya dace ya bayyana wanda ya lashe zaɓen.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: INEC ta bayyana Gwamna Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Adamawa | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kotu

Kotu ta soke zaɓen Gwamna Lawan na Zamfara

Published

on

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta a ranar Alhamis ta soke nasarar Da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal na jam’iyyar PDP ya samu.

A sakamakon haka, kotun ta bayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba.

Kotun dai ta ce za a sake zaɓen ne a wasu ƙananan hukumomin Jihar guda uku.

Ƙananan Hukumomin su ne Maradun da Birnin-Magaji da kuma Bukyun.

A cewar kotun, hukuncin da Kotun sauraron ƙararrakin zaɓen Gwamnan ya yi a baya, wanda ya tabbatar da nasarar Dauda, bai yi la’akari da hujjar da jam’iyyar APC mai ƙara ta gabatar ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Lawan ya amince da naira biliyan huɗu don gyara hanyoyi a Gusau

Kazalika, kotun ta yi fatali da sakamakon da APC da kuma Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) ta bayar a ƙaramar Hukumar Maradun.

Tsohon Gwamnan Jihar, kuma ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Muhammad Matawalle ne dai ya shigar da ƙarar yana neman a soke nasarar Dauda a zaɓen.

Hukumar INEC dai ta bayyana Dauda Lawal na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen na ranar 18 ga watan Maris din da ya gabata.

Continue Reading

INEC

INEC ta bayyana Uzodinma a matsayin wanda ya lashe zaɓen Imo

Published

on

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana Gwamna Hope Uzodinma na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Imo da aka gudanar a jiya Asabar.

Abayomi Sunday ,jami’in hukumar zaɓe ta INEC daga cibiyar tattara sakamakon zaɓen jihar dake Owerri, ne ya bayyana wanda ya lashe zaɓen a safiyar yau Lahadi.

Hope Odidika Uzodinma ɗan takarar APC ya samu ƙuri’u 540,308 inda ya kayar da abokin hamayyarsa na jam’iyyar PDP, Samuel Anyanwu, wanda ya samu ƙuri’u 71,503 yayin da ɗan takarar jam’iyyar Labour, Athan Achonu, ya zo na uku da ƙuri’u 64,081.

KU KUMA KARANTA: Matasa a Imo sun kama ɗan sanda bisa zargin sace ƙuri’un zaɓe

Hukumar zaɓen Najeriya ganin cewa Hope Odidika Uzodinma ya cika dukkan ka’idojin a ɓangaren da ya shafi doka,banda haka ya kuma samu rinjayen ƙuri’un da suka dace, an ayyana shi a matsayin wanda aka zaɓa.

Continue Reading

Labarai

Matasa a Imo sun kama ɗan sanda bisa zargin sace ƙuri’un zaɓe

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce za ta gudanar da bincike kan zargin tafka maguɗi a zaɓen da aka yi wa ɗaya daga cikin jami’anta a jihar Imo.

Bidiyon wani jami’in da wasu matasa ke riƙe da shi da suka zarge shi da sace ƙuri’a a cibiyar tattara ƙuri’u ta Amakohia Ikeduru a lokacin zaɓen gwamna da aka yi a ranar 11 ga watan Nuwamba.

Da yake mayar da martani ga faifan bidiyon, kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce;

‘’Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta na sane da zargin da ake yi wa wannan ɗan sanda da ake zargin yana da hannu wajen sace ƙuri’u a cibiyar tattara ƙuri’u ta Amakohia Ikeduru da ke jihar Imo. 

KU KUMA KARANTA: ’Yan daba sun buɗe wa masu zaɓe wuta a Bayelsa

Ba mu ɗauki wannan batu da wasa ba domin yana damun sahihancin rundunar da kuma yadda mambobinta za su iya tabbatar da ingancin zaɓe. 

Don haka muna tabbatar wa jama’a cewa za a gudanar da cikakken bincike, kuma za mu yi muku bayani nan da nan.  Yana buƙatar cikakken bincike.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like