Connect with us

Labarai

An fara gudanar da taron ƙungiyar yaɗa labaran Afirka karo na 14 a Abuja

Published

on

An samu mahalarta taron daga ƙasashen duniya daban-daban ciki har da Amurka. Taron zai duba abubuwa da dama kama daga gudumawar da kafafen yaɗa labarai su ke bayarwa wajen inganta cinikayya da ƙalubalen yaɗa shirye-shirye a yanayi na na’ura mai aiki da ƙwaƙwalwa da kuma dijital ko lataroni.

Taken taron na bana shi ne “Tasiri da ƙalubalen yaɗa labarun Afirka a cikin sauyin dijital na duniya”. Taro ne da gamayyar ƙungiyoyin yaɗa labarai a Afirka ta shirya tare da haɗin gwiwar hukumar Talabijin ta Najeriya wato NTA.

Wanan taro zai ba da dama a fahimci halayen kafofin yaɗa labaru na Afirka ta manyan batutuwan dijital da ke canja duniya. Hakan zai bai wa ‘yan kasuwa, manyan manajoji, malamai da masana damar yin aiki kan samar da arziƙi a ɓangaren yaɗa labarai.


A jawabinsa, Salihu Abdulhamid Dembos, shugaban Hukumar Talabijin ta ƙasa a Najeriya (NTA), ya yi bayani cewa kowace shekara ana gudanar da irin wannan taron wanda yake haɗa kan shugabannin gidajen yaɗa labarai na Talabijin da rediyo daga dukkannin sassan ƙasashen Afirka, inda sukan yi bitar ƙalubaloli da nasarorin da nahiyar Afirka ta ke samu ta fannonin yaɗa labarai.

KU KUMA KARANTA: Ranar ‘yan jarida ta ƙasa: Za mu bada goyon baya wajen yaɗa sahihancin labarai da kare ‘yancin ‘yan jarida – Kwamared Rajab

Abdulhamid ya ƙara da cewa, an samu koma baya a nahiyar Afirka ta fannin ƙirƙira, kuma saboda haka ne aka gayyato baƙi daga ƙasashen waje irin su nahiyar Turai, da Amurka, da ƙasar Rasha inda za su tattauna hanyoyin samun nasarori masu muhimmanci a nahiyar.

A nasa ɓangaren kuma, shugaban Hukumar da ke kula da kafafen yaɗa labarai ta ƙasar Najeriya Balarabe Shehu Ilella, ya yi nazarin taron inda ya ce yana da muhimmanci sosai domin za a yi ƙoƙarin canza yadda wasu ƙasashe suke kallon Afirka, domin a yanzu taron ya nuna cewa an ƙara samun zaman lafiya da haɗin kai a Nahiyar Afirka saɓanin yadda ake kallon nahiyar.
Balarabe ya ce nahiyar tana da ƙalubalen kayan aiki na zamani, saboda haka za a yi musayar ra’ayi wajen samun sabbin hanyoyin amfani da basirar ƙasashen da suka ci gaba.

Ɗaya daga cikin manyan baƙin da suka halarci taron kuma babbar darakta mai kula da sashin Afirka na Muryar Amurka Malama Salwa Jaafari ta bayyana farin cikin kasancewarta a wannan taron kuma ta ji daɗin gayyatar ta da aka yi. Salwa ta ce wannan wata dama ce da za ta haɗu da mutane daban-daban da suke da manufa iri ɗaya kuma masu wakilcin kafafen yaɗa labaru daban-daban daga ƙasashen duniya.

Salwa ta ce ta haɗu da mutanen da za ta iya hulɗa da su wajen yaɗa shirye-shiryen Muryar Amurka. Salwa ta ce abu na farko shi ne tattauna yadda ayyukan kafafen yaɗa labarai ke komawa na zamani. Ta ce wannan abu ne da zai zama mata abin alfahari da kuma jin daɗi ganin yadda ta samu karɓuwa wajen abokan aiki a Najeriya da na ƙasashen Afirka baki ɗaya.

Za a ci gaba da shirya irin wannan taron har ma za a shirya wani gagarumin baje kolin masu fasaha daban-daban daga sassa daban-daban na nahiyar a bainar baƙi na musamman.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like