Connect with us

Labarai

Akwai barazanar ambaliyar ruwa a jihohi takwas a Najeriya – NEMA

Published

on

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA, ta ce akwai yiyuwar ambaliyar ruwa a jihohin Adamawa, Taraba, Benuwe, Nasarawa, Kogi, Anambra, biyo bayan buɗe ruwa daga madatsar Lagdo da ke ƙasar Kamaru.

Mustapha Ahmed, Darakta Janar na NEMA, wanda ya bayyana hakan a taron ƙungiyar agajin gaggawa ta ƙasa, ranar Laraba a Abuja, ya ce wasu sun haɗa da jihohin Enugu, Edo, Delta, Ribas da Bayelsa.

Ya ce tilas ne jihohin da suke a can ƙasa su fara ɗaukar matakan da suka dace don magance tare da daƙile illolin da ke tafe da ambaliyar ruwa.

A cewarsa, taron ya wajabta ne bisa sanarwar da aka samu daga ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, kan yadda aka tsara sakin ruwa daga Dam ɗin Lagdo da ke Kamaru.

Ya ce ƙasar ta fara fitar da ruwa daga madatsar ruwa a kan mita 200 a cikin daƙiƙa ɗaya wanda ya kai kimanin mita 18 na ruwa a kowace rana.

KU KUMA KARANTA: Minista ta yi hasashen ambaliyar ruwa a wasu jihohi

Ya ce sakin na iya haifar da ambaliyar ruwa ga duk jihohin da ke kan gaba a cikin kwanaki da makonni masu zuwa.

“Jihohin da ke gefen kogin Benuwe sune Adamawa, Taraba, Benue, Nasarawa, Kogi, Anambara, Enugu, Edo, Delta, Rivers da Bayelsa.

“Bayanan da aka samu daga matakin ruwan kogin Benuwe a tashar auna ma’aunin ruwa ta Najeriya (NIHSA) da ke Makurɗi ya tsaya a mita 8.97 a ranar 25 ga Agusta, 2023 idan aka kwatanta da mita 8.80 a daidai wannan ranar a shekarar 2022.

“Har ila yau, NIHSA ta tanadi cewa tsarin kogin Neja, musamman a Niamey, Jamhuriyar Nijar, ya kasance mai ƙarko a daidai matakin da ya kai mita 4.30.

“Hakazalika, madatsun ruwa na cikin gida da suka haɗa da Kainji, Jebba da Shiroro sun ba da rahoton tsarin gudanar da kwarara,” in ji shi.

Babban daraktan ya ƙara da cewa, gaggawar kwashe ‘yan Najeriya daga al’ummomi daban-daban zuwa wurare masu aminci ya kamata duk masu ruwa da tsaki su aiwatar da su domin daƙile yiwuwar aukuwar ambaliyar ruwa a bana.

Sai dai ya yi ƙira ga ‘yan Najeriya da su kwantar da hankulan su domin hukumar za ta ci gaba da haɗa kai da abokan hulɗar gwamnati wajen samar da tallafi da suka haɗa da abinci da kayan abinci ga mutanen da abin ya shafa a sansanonin ‘yan gudun hijira da kuma al’ummomin da suka karɓi baƙuncinsu.

Tun da farko, Daraktan Tsare-tsare, Bincike da Hasashen Hukumar NEMA Dakta Onimode Bandele, ya ce an ƙira taron ne domin sabunta bayanai tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban kan batutuwan da suka shafi sakin ruwa daga Dam Lagdo da kuma halin da ake ciki a ƙasar nan.

Ya ce yana da mahimmanci a nemi gudunmawar su mai ma’ana a wasu don tsara hanyoyin da za a bi don magance matsalolin da za a iya fuskanta, shirya, ragewa da kuma mayar da martani ga matsalolin jin ƙai da sakin ruwa zai iya haifarwa.

A nasa jawabin, Clement Nze, Darakta Janar na NIHSA, ya ce yana da matuƙar muhimmanci a samar da babban shiri a ɓangaren gwamnatin tarayya da na jihohi, musamman a jihohin da abin ya shafa.

Ya ƙara da cewa, dole ne ‘yan ƙasar da suka haɗa da dukkan hukumomi da masu ruwa da tsaki da aka ɗorawa alhakin magance bala’o’i da raguwa, dole ne su ƙara ƙaimi tare da samar da matakan daƙile bala’in ambaliyar ruwa.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Mutane sama da dubu biyu ne suka mutu a Libya, sakamakon ambaliyar ruwan sama | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Za a fuskanci ambaliyar ruwa a jihohi 13, a Arewacin Najeriya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like