HomeKotuKotu ta soke...

Kotu ta soke rajistar jam’iyyar NDC

Babbar kotun tarayya da ke Lokoja a jihar Kogi ta soke hukuncin da ta yanke a baya wanda ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta yi wa jam’iyyar NDC rajista a matsayin jam’iyyar siyasa kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Mai shari’a Isah Dashen ya yanke hukuncin ne a ranar Juma’a, inda ya ce dole ne a saurari dukkan bangarorin da abin ya shafa kafin a yanke hukunci a kan lamarin.

Kotun ta amince da bukatar jam’iyyar PMP, wadda ta ce tana da ruwa da tsaki a shari’ar. Alkalin ya bayyana cewa hukuncin da aka yanke a watan Disamban 2025 ya samu nakasu saboda ba a saurari dukkan masu ruwa da tsaki ba.

Kotun ta umarci a mayar da al’amura yadda suke kafin hukuncin da aka yanke a ranar 10 ga Disamba, 2025, tare da ba da umarnin a sake fara sauraron shari’ar daga farko.

Lauyan PMP, Chikezie Ekeocha, ya ce jam’iyyar ta garzaya kotu ne bayan gano cewa NDC ta yi amfani da tambarin da PMP ta gabatar wa INEC tun kafin a fara shari’ar.

Ya bayyana cewa hukuncin kotun na nufin dakatar da duk wani mataki da INEC ta dauka dangane da rajistar NDC, ciki har da takardar rajista da sanya jam’iyyar cikin bayanan hukumar, har sai an kammala shari’ar.

Sai dai lauyan ya jaddada cewa har yanzu ba a yanke hukunci na karshe a kan shari’ar ba, domin kotun ta bukaci a hada dukkan bangarorin da abin ya shafa kafin ta sake yanke sabon hukunci.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Obi ya bukaci Tinubu ya dakatar da shirin kafa ‘yasandan jihohi sai bayan zaɓen 2027

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Tinubu da ya dakatar da aiwatar da tsarin kafa ‘yansandan jihohi har sai bayan babban zaɓen shekarar 2027. Obi ya bayyana haka ne bayan majalisar dokoki ta...

NANS Shiyya ta Arewa Maso Yamma da NEARLS Sun Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna ta Shekaru Uku

Daga Idris Umar, Zaria Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya (NANS) Shiyya ta A (Arewa maso Yamma) da National Agricultural Extension and Research Liaison Services (NEARLS) sun rattaba hannu kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna (MoU) ta tsawon shekaru uku domin bunƙasa kasuwancin noma, ƙarfafa...

Shugaba Tinubu, ya shawarci ‘yan Najeriya da su sanya idanu kan yadda gwamnatocin jihohi da na ƙananan hukumomi ke kashe kuɗaɗe

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci kafafen yada labarai su rika sanya ido ga jihohi da kananan hukumomi kan yadda suke amfani da kudaden da suke karba daga gwamnatin tarayya. Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.