Connect with us

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Matar da ta fi tsufa a duniya ta rasu

Published

on

Matar da ta fi tsufa a duniya ta rasu

Matar da ta fi tsufa a duniya ta rasu

Matar da ta fi kowa tsufa a duniya, ‘yar kasar Spain, Maria Branyas Morera, wacce aka haifa a Amurka kuma ta ga ‘yan duniya biyu, ta mutu tana da shekaru 117, in ji danginta.

“Maria Branyas ta bar mu. Ta mutu kamar yadda ta yi fata: wato a lokacin da take barcinta, cikin kwanciyar hankali kuma ba tare da jin raɗaɗi ba,” kamar yadda danginta suka rubuta a shafinta na X a ranar Talata.

“Za mu riƙa tunawa da ita saboda nasiharta da kyautatawarta,” in ji su.

KU KUMA KARANTA: Tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, Issa Hayatou, ya rasu

Branyas, wacce ta rayu tsawon shekaru 20 da suka gabata a gidan kula da tsofaffi na Santa Maria del Tura da ke garin Olot a arewa maso gabashin Spain, ta yi gargadi a cikin sakon da ta wallafa cewa tana jin “raunana”.

“Lokacina ya kusa. Kada ku yi kuka, ba na son a zubar min hawaye. Kuma kar ku wahalar da ni. Duk inda na je, zan yi farin ciki,” ta faɗa a shafin nata wanda iyalanta ke kula da shi.

Guinness World Records a hukumance ya amince da matsayin Branyas a matsayin wadda ta fi kowa tsufa a duniya a cikin watan Janairun 2023 bayan mutuwar Bafaranshe Lucile Randon mai shekara 118.

Bayan mutuwar Branyas, mutumin da ya fi kowa tsufa a duniya shi ne Tomiko Itooka dan kasar Japan, wanda aka haife shi a ranar 23 ga Mayun 1908 kuma yana da shekaru 116 a duniya, a cewar ƙungiyar bincike kan tsofaffi ta Amurka.

Maria Branyas Morera ta ce tsawon rayuwar da ta samu yana da alaƙa ne da rashin ɗaukar rayuwa da zafi da kula da lafiyar ƙwaƙwalwarta da ta jiki da kuma yin alaƙa mai kyau da mutane.

A yanzu bayan mutuwar Branyas, wani ɗan Japan Tomiko Itooka mai shekara 116 ne zai zama mutum mafi tsufa a duniya.

Continue Reading

Labarai

Za mu shiga yajin aiki matuƙar wani abu ya sami shugabanmu – NLC

Published

on

Za mu shiga yajin aiki matuƙar wani abu ya sami shugabanmu - NLC

Za mu shiga yajin aiki matuƙar wani abu ya sami shugabanmu – NLC

Daga Idris Umar, Zariya

Shugabancin ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta yi barazanar yin watsi da duk wasu kayan aiki a duk faɗin ƙasar idan rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tsare shugabanta, Comrade Joe Ajaero.

Kungiyar ta yi wannan barazanar ne a safiyar ranar talata a hedkwatarta, jim kaɗan bayan gudanar da taron gaggawa na Majalisar Zartarwa ta ƙasa, domin tattaunawa kan gayyatar da ‘yan sanda suka yi wa Shugaban NLC, kan zargin tallafa wa ayyukan ta’addanci.

Hukumar ta NEC ta yanke shawarar cewa Ajaero ya mutunta gayyatar da ‘yan sanda suka yi masa amma ya lura cewa mai ba su shawara kan harkokin shari’a ya nemi ƙarin lokaci domin Shugaban NLC ya gurfana gaban hukumar ‘yan sanda.

Kwamared Ado Kabiru Sani, mataimakin shugaban ƙungiyar NLC, ya buƙaci ma’aikatan ƙasar nan da su kasance cikin shirin ko ta kwana domin samun ƙarin umarni idan ‘yan sanda suka yi abin da ya saba tsammanin tsare Ajaero.

KU KUMA KARANTA: Zanga-Zanga: DSS ta musanta kai samame ofishin NLC

A cewarsa “A matsayinmu na cibiyar ƙwadago, za mu mutunta gayyatar da ‘yan sanda suka yi mana, domin mu ba ƙungiyar da ba ta da fuska ba ce, amma muna aiki da lauyanmu na tsawon lokaci.

“Idan aka kama shugaban mu na ƙasa, duk ma’aikata za su sauƙe kayan aiki nan take.  Ya kamata mu jira ƙarin umarni daga shugabanninmu.”

Continue Reading

Labarai

Mata da miji sun damfari al’umma sama da miliyan 80 a Kano

Published

on

Mata da miji sun damfari al'umma sama da miliyan 80 a Kano

Mata da miji sun damfari al’umma sama da miliyan 80 a Kano

Wasu mata da miji da suka zo garin Bebeji a jihar Kano, suka kama gidan haya suka zauna, mijin ya nemi aikin kamfani a garin sun kai kusan shekara uku, sai suka fara sai da taliya.

A hankali ana zuwa ana saya akan farashi mai sauƙi har ta kai ga mutane ba sa iya sayan taliya a wani gurin sai wajensu, suna sayar da taliya duk guda ɗaya akan naira 600 in kuma a shago ne zaka saya nai ɗari 750 ko sama da haka.

Wannan sauƙin ne ya sa mutane suke tururuwa har da daga wasu garuruwa ana zuwa saya ko mota ɗaya aka kawo a nan take yake ƙarewa.

A hakan wasu ma ba sa samu, sai mutane suka koma ba da kuɗi kafin a kawo taliyan.

Za a ɗauki sunanka idan an kawo duk wanda ya ba da kuɗi ana ƙiran suna a ƙarshe dai ta kai ta kawo tun kafin a kawo za ka ba da kuɗin ka in an kawo sai a ba ka, akwai masu ba da miliyan 4, 5, da dai masu dubun nan ɗarurruka.

KU KUMA KARANTA: Makaho ya damfari wata mata naira miliyan 19, ya yi lalata da ‘yarta da jikarta

A yanzu haka wannan mata da mijinta jiya sun gudu anne mesu an rasa. Sun tafi da kuɗin da ana zaton sun fi million 80.

Muna ƙira ga Jama’a sai a kula ka da wasu su zo garinku da irin wannan dan indai haka suke yi tabbas za su iya zuwa wani garin, sai an saba dasu daga ƙarshe su damfari mutane su gudu. Ubangiji Allah ya kiyaye.

Majiya Tsumagiya ta Kwafoshi

Continue Reading

You May Like