Connect with us

Labarai

Yaran Najeriya sun cancanci samun ilimi cikin kwanciyar hankali – UNICEF

Published

on

Asusu tallafa wa ƙananan yara na majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya yi Allawadai da harin baya-bayan nan da aka kai kan wata makaranta a jihar kaduna.
A sanarwar da ya fitar a ranar Juma’a, wakilin UNICEF a Najeriya, Christian Munduate, ya bayyana takaici game da harin, inda yace yaran Najeriya sun cancanci samun ilimi a yanayi na lumana.

Wakilin asusun na UNICEF ya ƙara da cewar, kamata ya yi makarantu su kasance killatattun wurare na neman ilmi da ci gaba amma ba bigirorin tsoro da tashin hankali ba.

An ruwaito sanarwar na cewa, “na yi matuƙar baƙin ciki da damuwa game da wannan rahoto na sake sace ɗalibai a jihar Kaduna. Yawaitar irin waɗannan al’amura a faɗin Najeriya alama ce ta tashin hankalin da ke buƙatar ɗaukar matakan gaggawa masu tsauri daga dukkanin matakan gwamnati da al’umma. Kamata ya yi makarantu su zama keɓaɓɓun wuraren neman sani da ci gaban ɗan adam, amma ba bigirorin tsoro da tashin hankali ba”.

KU KUMA KARANTA:Ɗalibi ɗaya ya kuɓuta daga cikin ‘yan makarantar da ‘yan bindiga suka sace a Kaduna

“Satar ɗalibai na baya-bayan nan, kamar waɗanda suka gabace shi, abin allawadai ne kuma wani ɓangare ne na salon kai hare-hare akan cibiyoyin ilimi, musamman ma a shiyyar arewa maso yammacin Najeriya, inda ƙungiyoyin ‘yan bindiga suka zafafa kai hare-hare da yin garkuwa da mutane. Kwana guda kafin aukuwar wannan lamari, jami’in Majalisar Ɗinkin Duniya a Najeriya ya zanta akan satar ɗimbim mata da ‘yan mata harma samari da mayaƙan ƙungiyar Boko Haram suka yi a jihar Borno”.

“Asusun tallafawa ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, da haɗin gwiwar wasu jami’an Najeriya na taimakawa wajen kwantar da hankulan iyaye da dangin yaran da aka sace.

UNICEF ya duƙufa wajen yin haɗin gwiwa da gwamnatoci da al’umma da ƙungiyoyin ba da agaji domin magance dalilan da ke jefa yara cikin tashin hankali tare da ba da kariya ga makarantu daga kowace irin barazana da tashin hankali.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like