Connect with us

Labari

Abubuwan da ba ku ji ba game da ƙasar Mozambik (Hotuna)

Published

on

Mozambik, ƙasa ce da ke kudu maso gabashin Afirka, ta na kuma da iyaka da Tekun Indiya daga gabas, Tanzania a arewa, Malawi da Zambiya a arewa maso yamma, Zimbabwe a yamma, da Eswatini da Afirka ta Kudu a kudu maso yamma.

Ƙasar ta na da babban teku da ke da mahimmanci ga tattalin arziƙin ƙasar da kuma rawar da yawon buɗe ido da kamun kifi ke taka wa wajen ci gaban ƙasar.

Ƙasar mai cin gashin kanta a halin yanzu, an raba wani yanki daga cikinta zuwa Comoros, Mayotte da Madagascar ta tashar ruwa na Mozambik da ke gabas.

Tsakanin ƙarni na 7 zuwa na 11, jerin garuruwan tashar jiragen ruwa na Swahili sun haɓaka a wannan yanki, waɗanda suka ba da gudunmawa ga haɓaka al’ada da harshen Swahili.

A ƙarshen zamanin da, ‘yan kasuwa daga Somaliya, Habasha, Masar, Saudi Arabiya, Parisa, da Indiya ne ke yawan zuwa waɗannan garuruwa domin fatauci.

Tsibirin Mozambik, wani yanki ne mai cike da murjani a gaɓar tekun ƙasar, kuma wani matsayi ne mai muhimmancin tarihi, inda al’adu daban-daban suka haɗu kuma suka bar tarihi a lokacin ɓullowa da bunƙasuwar hanyar cinikin teku tsakanin nahiyoyi a faɗin yankin.

Mozambik ta na da albarkatu masu tarin yawa, duk da cewa tattalin arziƙin ƙasar ya dogara ne a kan kamun Kifi, da noma tare da bunƙasa masana’antar abinci da abubuwan sha, masana’antar sinadarai, aluminum da man fetur. Sai dai kuma, ɓangaren yawon buɗe ido ya na ƙara faɗaɗa.

Yawan al’ummar ƙasar ya kai kusan miliyan 30, kamar yadda aka ƙiyasta a 2022, sun kuma ƙunshi ‘yan ƙabilar Bantu da dama.

Babban birnin ƙasar shi ne Maputo, wadda ya ke zama Fadar Gwamnatin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Jarirai na iya banbance sautin kalamai sa’o’i kaɗan bayan haihuwa

Haka nan, harshen hukuma ɗaya tilo a Mozambik shi ne harshen mulkin mallaka na Portuguese, wadda galibi ana magana da shi a cikin birane a matsayin harshe na farko ko na biyu, kuma gaba ɗaya a matsayin harshen gudanarwa na gwamnati.

Harsunan gida mafi mahimmanci sun haɗa da Tsonga, Makhuwa, Sena, Chichewa, da Swahili. Har ila yau, akwai kusan harsuna 46 da ake magana da su a cikin ƙasar, ɗaya daga cikin mafi shura shi ne, Língua de sinais de Moçambique.

Addini mafi girma a Mozambik shi ne, Kiristanci, tare da wasu tsiraru masu bin addinin Musulunci da kuma addinan gargajiya na Afirka.

Hukumar Kula da Adana Kayan Tarihi ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO), ta lissafa tsibirin a matsayin ɗaya daga cikin wuraren tarihi na duniya a cikin shekara ta 1991.

Kalli hotunan a nan:

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

Labari

Gwamna Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a Zamfara

Published

on

Gwamna Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a Zamfara

Gwamna Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a Zamfara

A ranar Alhamis, gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Suleiman Bala Idris, ne ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis, inda yace majalisar tsaron jihar ta yanke shawarar taƙaita zirga-zirgar baburan ne a yayin wani taron gaggawa da ya gudana a Larabar da ta gabata.

Gwamnan ya sanya hannu akan dokar ne a fadarsa da ke Gusau, babban birnin jihar.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Zamfara ya jinjinawa jami’an tsaro tare da yin jaje ga wanda iftila’in ya shafa

An ruwaito sanarwar na cewa, “yau, gwamna Dauda Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar da ke taƙaita ko haramta zirga-zirgar babura daga ƙarfe 8 na dare zuwa 6 na safiya a ko’ina a faɗin jihar.

“Hakan wani yunƙuri ne na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da daƙile kalubalen tsaro da fadada matakan da gwamnati ke ɗauka wajen yaƙi da matsalar ‘yan bindiga da sauran nau’ukan laifuffuka a jihar.

“An baiwa antoni janar na jihar zamfara ikon gurfanar da duk wanda ya sabawa dokar a gaban ƙuliya.”

Continue Reading

Labari

Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Published

on

Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Wannan mutumin ɗan Ghana ne, talaka ne, kuma yana zaune a ƙauye ne a wajen birni. Shekaru kaɗan da suka gabata wani jirgin sama mara matuƙi mallakar kamfanin dillancin labaran Turkiyya ya faɗo kusa da gidansa.

Da ‘yan jaridar ƙasar Turkiyya suka zo neman jirginsu, sai suka iske mutumin riƙe da jirgin mara matuƙi a hannunsa. Ya ce ga abinku, cikin raha ya tambaye su “kuna da wanda ya fi shi girma wanda zai kai ni aikin Hajji?”

Sai kuwa wani ɗan jarida ya wallafa labarin, daga nan kuma gwamnatin Turkiyya ta yanke shawarar tura mutumin Hajji ba tare da ya kashe ko sisin kwabonsa ba, wato dai duk abin da ake buƙata a tafiyar za ta biya masa.

KU KUMA KARANTA: Labarin Haji Hassan na ƙasar Iran

Ga shi nan dai a bana Allah Ya cika masa burinsa ya je Makkah domin aikin Hajjinsa.

Darasin labarin: Idan Allah ya ƙira ka zuwa Makkah, zai yi amfani da duk wani abu da duk wanda zai sa tafiyarka ta yiwu.
Allah ne mafificin tsari.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like