Connect with us

Labarai

Mataimakin shugaban ƙasa Shettima, ya ƙaddamar da manyan ayyuka a jihar Borno

Published

on

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya ƙaddamar da sabbin makarantu uku da cibiyar kula da lafiya a matakin farko da gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya aiwatar a cikin kwanaki 100 na ci gaba da wa’adinsa na biyu.

Shettima wanda ya isa Maiduguri a ranar Juma’a, ya samu tarba daga Gwamna Zulum, da shugabannin jam’iyyar APC, da manyan jami’an gwamnati a filin jirgin Muhammadu Buhari.

Sanata Shettima ya fara aikin nasa ne a makarantar Shuwari II Mega Primary School, wadda ke da ajujuwa 20 masu ɗaukar aƙalla ɗalibai 1,200.

Makarantar kuma tana da wuraren shaƙatawa na ma’aikata da wuraren wasanni.

KU KUMA KARANTA: Jihohin Borno, Adamawa, da Yobe, sun cire tallafin sufuri ga ma’aikata da ɗalibai

Haka kuma a Shuwari II, mataimakin shugaban ƙasar ya ƙaddamar da wata cibiyar kula da lafiya matakin farko mai gadaje 30, wadda aka gina domin magance ƙaruwar buƙatu na kiwon lafiya sakamakon kwararowar ‘yan gudun hijira a cikin birnin Maiduguri da kewaye.

Daga nan ne mataimakin shugaban ƙasar ya kai ziyarar ban girma ga Shehun Borno, Alhaji Dakta Abubakar Ibn Umar Garbai Al-Amin Elkanemi.

Daga fadar Shehu, mataimakin shugaban ƙasar ya je ‘commissioner day Secondary School’, Gamboru, mai sunan Marigayi tsohon sakataren gwamnatin jihar Borno, Usman Jidda Shuwa.

Makarantar tana da ajujuwa 30, wuraren wasanni, da ɗakunan gwaje-gwaje, a tsakanin sauran kayan aiki.

Sannan Shettima yaje ya buɗe wata makarantar mega a unguwar Alakaramti. Makarantar tana da ajujuwa 30, shingen gudanarwa, wuraren wasanni, wutar lantarki, da tsarin ruwa.

A wuraren da aka ƙaddamar da aikin, mataimakin shugaban ƙasa ya raba riguna, kayan rubutu, da litattafai ga ɗalibai.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Gwamnatin Borno ta rufe makarantu masu zaman kansu 300 | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like