Connect with us

Ƙasashen Waje

Sojojin Nijar sun amince su tattauna da ECOWAS

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Wasu bayanai na nuna cewa sojojin na Nijar a yanzu sun ɗan sassauto inda suka nuna alamun yarda su tattauna da ECOWAS.

A baya sojojin sun ƙi bayar da dama ga wata tawaga ta musamman da ECOWAS ta tura Nijar ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban mulkin soja na Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar domin tattaunawa.

A ranar Asabar majalisar dokokin ƙungiyar ta ƙasashen Afirka ta Yamma ta ce za ta tura wani kwamiti babban birnin Nijar ɗin Niamey.

Sai dai kuma ba ta sanar da ainihin lokacin da za ta tura kwamitin ba.

KU KUMA KARANTA: Ƙasar Rasha ta gargaɗi ƙungiyar ECOWAS game da ɗaukar matakin soji

Haka kuma a ranar Litinin ɗin ne kwamitin tsaro na ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU, kasashe 55 zai gana domin tattauna yanayin na Nijar.

Ana ganin wannan wata alama ce ta nuna damuwa kan wannan juyin mulki, wanda ya kasance na bakwai a tsakanin ƙasashen Afirka ta Yamma da Afirka ta Tsakiya a cikin shekara uku.

Wani abu da ke ɗaukar hankali a kan halin da nahiyar ke ciki dangane da juyin mulkin da ake samu shi ne ba wai makomar Nijar ba kaɗai, wadda kasa ce mai arziƙin sinadarin yureniyom, da kuma kasancewarta kawar ƙasashen Yamma a yaƙi da masu iƙirarin jihadi, akwai fargabar gogayya da ake samu da sauran manyan ƙasashen duniya abokan hammayyar Yamma, domin samun tasiri a nahiyar.

Ƙungiyar Tarayyar Afirka da majalisar Ɗinkin Duniya da kuma Tarayyar Turai dukkaninsu sun mara baya ga ECOWAS a kan duk matakin da za ta ɗauka na mayar da dimukuraɗiyya da kuma Shugaba Bazoum kan mulki.

Ƙungiyoyin har ma da Amurka sun nuna damuwa game da lafiyar shugaban kan halin da aka ce yana ciki, saboda yadda yake tsare.

A ranar Asabar ne wata tawaga ta shugabannin addinin Musulunci ƙarƙashin jagorancin Shaikh Bala Lau, na ƙungiyar Izala ta je Yamai domin tattauna batun na Nijar.

Tawagar wadda ta samu ganawa da sabon Firaministan da sojoji suka naɗa, Ali Mahaman Lamine Zeine, ta kuma samu ganawa da jagoran juyin mulkin wanda ya naɗa kansa sabon shugaban ƙasa Janar Abdourahamen Tchinai.

Bayanai sun nuna cewa tawagar ta shugaban na ƙungiyar Izala ta je Nijar ɗin ne bisa izinin ƙungiyar ECOWAS da kuma shugabanta wanda kuma shi ne shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, domin kwantar da hankali ganin yadda lamarin ke neman haifar da tashin-tashina saboda matakin soji da ECOWAS ke cewa za ta ɗauka.

Ganin yadda matakin da ECOWAS ta ɗauka na sanya wasu jerin takunkumai a kan Nijar ɗin na neman haifar da tsama tsakanin ƙasashen biyu, malaman sun nuna wa sojojin cewa wannan mataki ne na ƙungiya amma ba Najeriya ba, kamar yadda bayanai suka nuna.

A makon da ya gabata ne Sheikh Bala Lau da ‘yan tawagar tasa suka gana da Shugaba Tinubu a Abuja, inda bayanai suka ce a wannan zama ne aka tsara zuwa ganawa da shugabannin juyin mulkin na Nijar.

ECOWAS ta jaddada cewa har yanzu dukkanin wata ƙofa ta sasanta rikicin na Nijar a buɗe take, kuma matakin soji zai ci gaba da kasancewa zaɓi na ƙarshe idan komai ya ci tura.

Ministan harkokin waje na gwamnatin Nijar da sojojin suka hamɓarar, Hassoumi Massaoudou, yace matakin soji da ECOWAS ke cewa za ta ɗauka a kan masu juyin mulkin ba yaƙi ne a kan Nijar da ‘yan ƙasar ba, matakin tabbatar da doka ne a kan waɗanda ya ƙira masu garkuwa da mutane da masu taimaka musu.

Ƙasashen Waje

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Published

on

Dakta Mas'ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Dakta Mas’ud Pezeshkian ne lashe zaɓen shugaban ƙasar Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Waye Dakta Mas’ud Pezeshkian sabon shugaban ƙasar Iran na 9 cikin shekaru 45 ataƙaice?

An haife shi a ranar 29 ga Satumba, 1954, a Mahabad, a yammacin lardin Azarbaijan, Dakta Mas’ud Pezeshkian ya wakilci birnin Tabriz da ke arewa maso yammacin kasar a majalisar dokokin Iran ta 12.

Ya riƙe muhimmin muƙamai a majalisar a Hukumomi daban-daban matakin gwamnatin tarayya, kuma ya zama ministan lafiya a lokacin mulkin Shugaba Mohammad Khatami (2001-2005). Duk da cewa an tsige shi bayan wasu lokuta saboda gaza cimma wasu ayyuka da kawo sauyi.

An zaɓe Pezeshkian a majalissar 8th, 9th, 10th, and 11th. A tsakanin shekarar 2016 zuwa 2020, ya kuma rike mukamin mataimakin shugaban majalisar na farko. A baya dai ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2013 da 2021 amma ya kasa samun nasara a lokuta biyun.

KU KUMA KARANTA: An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Dr. Mas’ud Pezeshkian likitan zuciya ne kuma me koyarwa, ya yi aiki a matsayin shugabar Jami’ar Tabriz ta Kimiyyar kiwon lafiya, kuma a halin yanzu memba ne na ma’aikatan ilimi a wannan babbar jami’a a arewacin Iran.

Bayan da ya samu amincewa daga babbar hukumar da ke sa ido kan zabukan kasar na ya tsaya takara a zaben na ranar 28 ga watan Yuni a watan da ya gabata. Ya gabatar da tsare-tsarensa, inda ya jaddada muhimmancin damka ayyuka ga kwararru kuma masu ilimi a gwamnatinsa.

Haka nan kuma ya bayyana Javad Zarif, tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran a matsayin zabinsa na shugabancin ma’aikatar harkokin wajen kasar, yayin da ya sha alwashin aiwatar da umarnin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Pezeshkian a hukumance ya shiga takarar neman kujerar shugaban kasar a ranar 1 ga watan Yuni, rana ta uku ta rajista, a ma’aikatar harkokin cikin gida da ke Tehran, tare da rakiyar gungun magoya bayanta.

A muhawarar zagaye na biyu na zaben shugaban kasa, Pezeshkian ya bayyana mahimmancin kiyayewa da cika alkawura a matsayin wani muhimmin al’amari na kiyaye kyawawan halaye.

Ya jaddada muhimmancin nuna girmamawa ga daidaikun mutane, tabbatar da jin muryoyinsu, da bayar da shawarwari kan ayyuka bisa ka’idojin adalci da adalci.

Tsohon ministan lafiya ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da amana ke takawa wajen ciyar da al’umma gaba, tare da jaddada cewa gaskiya na da matukar muhimmanci wajen samar da amana a tsakanin al’umma.

Pezeshkian ya jaddada muhimmancin ba da fifiko kan dangantaka da kasashen dake makwabtaka da ita, da fadada huldar dake tsakanin kasashen duniya don bunkasa ci gaban kasar.

A lokuta da dama, ya nanata kudurinsa na mutunta tsarin dokokin Jamhuriyar Musulunci da kuma manufofin da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamene ya bayyana.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Published

on

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra'ila

Hezbollah ta harba rokoki 200 da jirage marasa matuƙa cikin Isra’ila

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ƙungiyar Hezbollah mai da ke Lebanon ta ƙaddamar da hare-haren rokoki fiye da 200 da jirage marasa matuƙa zuwa arewacin Isra’ila, a wani martani na kisan ɗaya daga cikin manyan kwamandojinta.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce an kashe sojanta da dama a hare-haren, na Hezbollah.

Sojojin na Isra’ila sun kuma ce sun mayar da martani kan mayaƙan ƙungiyar da sansanoninta da ke kudancin Lebanon.

Kafofin yaɗa labaran Lebanon sun ce mutum guda ya mutu a wani harin jirgi maras matuƙi da Isra’ila ta kai garin Houla.

Hare-haren na baya-bayan nan, sun kasance mafiya muni cikin watanni tara tsakanin kan iyakokin ƙasashen biyu.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

An kashe ɗaya daga cikin kwamandojin Hezbollaha wani hari ta sama da Isra’ila ta kai birnin Tyre na ƙasar Lebanon.

Mohammed Nimah Nasser, ya kasance ɗaya daga cikin manyan jagororin ƙungiyar, kafin kisan nasa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

Published

on

Wani jirgin ruwa ya kife da 'yan ci-rani a tekun Mauritania

Wani jirgin ruwa ya kife da ‘yan ci-rani a tekun Mauritania

‘Yan ci-rani kimanin 90 ne suka rasu a kan hanyarsu ta zuwa Turai a lokacin da jirgin ruwan da suke ciki ya kife a farkon makon nan a gabar tekun Mauritania, in ji kafar watsa labarai ta ƙasar wadda ta ambato jami’ai na bayani a ranar Alhamis.

Ana kuma ci gaba da neman da dama da suka bata.

“Jami’an tsaron teku na Mauritania sun gano gawawwakin mutane 89 da suka hau wani babban jirgin ruwan masunta da ya kife a ranar Litinin 1 ga Yuli a gabar tekun Atlantika,” kusan nisan kilomita huɗu daga gabar garin Ndiago a kudu maso-yammacin kasar, in ji kamfanin dillancin labarai na Mauritania a ranar Alhamis.

Jami’an tsaron iyakokin tekun sun kuma kuɓutar da wasu mutanen tara, ciki har da wata yarinya ‘yar shekara biyar, in ji kafar yaɗa labaran.

Kamfanin dillancin labaran ya rawaito cewa wadanda suka kuɓuta na cewa jirgin nasu ya taso ne daga iyakar Senegal da Gambia dauke da fasinja 170, wanda hakan ya sanya ake neman mutane 72 da suka ɓata.

Wani babban jami’in karamar hukuma a yankin da ya nemi a boye sunansa ya tabbatar wa AFP aukuwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Jirgin sojin Najeriya ya faɗo a Kaduna

Hanyar tekun Atlantika na da hatsari sosai saboda manyan igiyar ruwa, kuma ‘yan ci-rani na yin lodin da ya haura ka’ida a jiragen ruwa, a mafi yawan lokuta jiragen ba su da ingancin shiga teku, kuma ba sa ɗaukar isassen ruwan sha.

Amma hakan ya sake fitowa fili ne sakamakon yadda ake ƙara sanya idanu kan tekun Bahar Rum.

A shekarar 2023 adadin ‘yan ci-rani da suke zuwa tsibiran Canary na Sifaniya ya ninka a shekara guda, wanda ya kai mutane 39,910, kamar yadda gwamnatin Sifaniya ta bayyana.

Tsibiran Canary na Sifaniya na daura da iyakar tekun arewacin Afirka da nisan kilomita 100.

Amma jiragen ruwa da dama – mafi yawansu na katako – na kama hanya daga Maroko, Yammacin Sahara, Mauritania, Gambia da Senegal don zuwa tsibiran na Sifaniya.

Sama da ‘yan ci-rani 5,000 ne suka mutu a teku yayin ƙoƙarin tsallaka wa Sifaniya a watanni biyar na farkon wannan shekarar, kenan mutane 33 ne ke mutuwa kowacce rana, kamar yadda Caminando Fronteras, wata ƙungiyar bayar da agaji ta Sifaniya ta bayyana.

Wannan ne adadin rasa rayuka mafi yawa tun bayan da kungiyar ta fara tattara bayanai a 2007, kuma mafi yawa na mutuwa ne a hanyar tekun Atlantika.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like