Ƙasashen Waje
An tabbatar da Sojoji sun yi juyin mulki a Nijar
Daga Ibraheem El-Tafseer
Sojoji sun sanar da karɓe iko a Nijar a hukumance.
Wasu sojoji ƙalilan ne suka fito gidan talabijin na ƙasar suka tabbatar da juyin mulkin da suka yi.
Kakakin sojojin ƙasar Manjo Ahmadou Abdrahamane ne ya sanar da juyin mulkin.
Sun sanar da rushe kundin tsarin mulkin ƙasar, sannan kuma sun kulle duka iyakokin ƙasar baki ɗaya.
Babu dai labarin halin da Mohamed Bazoum ke ciki ya zuwa yanzu.
KU KUMA KARANTA: Ba za mu lamunci yunƙurin juyin mulki a Nijar ba – ECOWAS
Amma sojojin sun bayar da sanarwar sun tuɓe shi daga muƙaminsa.
Sun ce sun yi juyin mulkin ne saboda halin da Nijar ke ciki na taɓarɓarewar tsaro da tattalin arziƙi.
Sun kuma sanar da dokar hana fita daga ƙarfe 10 dare zuwa 6 na safe.
Shugaban ƙasar Benin Patrice Talon wanda ke jagorantar tawagar ECOWAS na cikin ƙasar, sai dai sun gaza cimma wata yarjejeniya da masu gadin shugaban ƙasar da suka amshe mulkin.
Tun a safiyar jiya Laraba ne aka bayar da rahotannin tsare Shugaba Bazoum a gidan gwamnati, abin da ya janyo zanga-zanga daga magoya bayan Bazoum.
Sojoji sun yi harbe-harben jan kunne domin tarwatsa masu zanga-zangar.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya nuna rashin goyon bayan wannan ƙasarsa kan juyin mulkin.
Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres ya ce ya yi magana da Shugaba Bazoum kuma ya tabbatar masa da cewa yana da goyon bayan Majalisar.
Wannan ne juyin mulki na huɗu da aka yi a Nijar tun bayan samun ‘yancin kai da ta yi daga Faransa a 1960, kuma an ta yin yunƙurin junyin mulki da yawa a ƙasar da ba su yi nasara ba.
Ƙasashen Waje
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali
Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.
Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.
Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.
KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai
Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.
Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.
Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.
Ƙasashen Waje
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila
Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.
Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.
KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan
Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.
Ƙasashen Waje
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan
Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.
A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”
Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.
Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.
Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.
KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD
Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: Na yi mamakin juyin mulki a jamhuriyar Nijar – Buhari | Neptune Prime Hausa
Pingback: Sojojin Nijar na zargin Faransa na shirin kai hari don kuɓutar da Bazoum | Neptune Prime Hausa
Pingback: Sojojin Nijar na zargin Faransa na shirin kai hari don kuɓutar da Bazoum - LEGEND FM DAURA