Connect with us

Labarai

Wasu jihohi a arewacin Najeriya za su fuskaci ƙarancin ruwan sama – NEMA

Published

on

Jihohin Kaduna, Kano, Bauchi, Jigawa, Yobe da birnin tarayya Abuja za su iya fuskantar ƙarancin ruwan sama.

Babban Darakta na Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa, NEMA, Mustapha Ahmed ne ya bayyana haka, cewa “babban birnin tarayya, Abuja, Kaduna, Bauchi, Kano, Jigawa da Yobe na iya samun ƙarancin ruwan sama a cikin wannan shekara”.

Ya bayyana hakan ne a wajen taron shirye-shiryen fuskantar dɗmatsaloli da sauyin yanayi na shekarar 2023, ranar Alhamis a Abuja.

KU KUMA KARANTA: Yadda ruwan sama ya lalata gidaje sama da ɗari a Ekiti

Ya ce ana sa ran Bayelsa, Akwa-Ibom, Delta da Cross River za su samu ruwan sama mai girman 2700mm zuwa sama. Malam Ahmed ya ce bisa la’akari da hasashen ambaliyar ruwa na shekara ta 2023 da Hukumar Kula da Ruwa ta Najeriya, NIHSA ta fitar, ƙananan hukumomi 66 na fuskantar haɗarin ambaliya a watannin Afrilu zuwa Yuni.

Ya ce ƙananan hukumomi 148 ne za su kasance cikin haɗarin ambaliya a watannin Yuli zuwa Satumba, yayin da wasu 100 kuma a watannin Oktoba da Nuwamba za su haɗu da ambaliyar.

“Bugu da ƙari, jimillar ƙananan hukumomin guda 41 sun faɗa cikin matsakaitan wuraren haɗarin ambaliya a cikin watannin Afrilu zuwa Yuni. Ƙananan hukumomi 199 a watannin Yuli zuwa Satumba, da kuma ƙananan hukumomi 72 a watannin Oktoba da Nuwamba.

“Hasashen na bana ya nuna cewa akwai babban haɗarin ambaliya a bakin teku saboda hasashen da ake sa ran za a yi a matakin ruwan teku da magudanar ruwa da ka iya yin illa ga noma, matsugunan mutane da sufuri a jihohin Bayelsa, Delta, Legas da Rivers.

“An kuma yi hasashen ambaliyar ruwa da ambaliyar ruwa a birane da garuruwa da yawa saboda rashin tsarin magudanar ruwa da rashin bin ƙa’idojin tsare-tsare da muhalli,” in ji shi.

Babban daraktan ya ce, bisa hasashen da aka yi, shekarar na iya ganin ambaliyar ruwa kwatankwacin abin da ya faru a bara, idan ba haka ba.

A cewar Ahmed, hukumar ta rubuta wasiƙu zuwa ga gwamnatocin jihohi 36 da kuma gwamnatin babban birnin tarayya Abuja domin sanar da su ƙananan hukumomin da ke cikin haɗari da matakan da ake sa ran za su ɗauka.

Hukumar, in ji shi, ta kuma fara wayar da kan jama’a kan buƙatar yin biyayya ga gargaɗin farko daga dukkan ‘yan Najeriya.

Ya shawarci ’yan Najeriya da su yi watsi da sauye-sauyen yanayi don rage haɗarin bala’i tare da ɗaukar duk shawarwarin da hukumomin da abin ya shafa suka fitar.

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like