Connect with us

Labarai

Yadda ƙarancin naira ya haddasa rikici a Ogun

Published

on

Tsoro ya dabaibaye mazauna garin Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, da ‘yan kasuwa, yayin da wasu fusatattun matasa suka gudanar da zanga-zanga a sassa da dama na babban birnin jihar.

Rahotanni sun ce an fara zanga-zangar ne a yankin Asero a Abeokuta, a ranar talata, da wasu abokan hulɗar bankin GTBank suka yi kan rashin samun sabbin takardun kuɗi na Naira daga bankin.

Masu zanga-zangar da suka yi tashe-tashen hankula a kan tituna sun tare hanyar da ta nufi Adatan da Osiele zuwa Ibadan a yayin zanga-zangar.

Haka kuma zanga-zangar ta bazu zuwa Adatan, Sapon, Oke-Ilewo, Lafenwa da dai sauransu, inda jama’a suka yi ta rataye ganye a jikin ababan hawansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Lanre Bankole, ya yi gaggawar garzayawa wurin da lamarin ya faru domin kwantar da hankulan da ya tilastawa jami’an bankin dakatar da ayyukansu.

KU KUMA KARANTA: CBN zai hukunta duk bankunan da ke ɓoye sabbin kuɗi

An kuma ɗauki matakin ne a lokaci guda yayin da wasu matasa da suka fusata suka je Sapon, Lafenwa, Adatan, Gbonagun Obantoko inda suka gudanar da zanga-zangar.

Wani banki a Sapon ya dakatar da aikinsa ba tare da bata lokaci ba don gudun kada a kai masa hari yayin da bankunan Oke-Ilewo da Panseke suma suka rufe ofisoshinsu kafin fusatattun matasan su far musu.

An ga wasu ma’aikatan bankunan a Oke-Ilewo da Panseke sun fice daga harabar da gudu, daga bisani matasan sun isa Oke-Ilewo inda suka lalata duk wasu kayan ‘yan siyasa da suka rataya akan fitilun kan titi.

Matasan da ke tafiya a kan babura sun kuma tare hanyar Lalubu a yayin zanga-zangar, inda suka hana zirga-zirgar ababen hawa, sun yi ta harbe-harbe a wasu wurare yayin da ba a ga ’yan sanda ba sai bayan fusatattun matasan sun bar wurin.

Haka kuma wasu masu zanga-zangar sun kai farmaki wani reshen bankin First Bank da ke Lafenwa a Abeokuta inda suka lalata na’urar tantance motoci da ke bankin.

An kuma bayyana cewa an rufe makarantu sakamakon ruɗanin da aka samu yayin da aka kai hari wata makarantar sakandare dake Gbonagun, Obantoko.

Wani malami a makarantar da ya nemi a sakaya sunansa ya ce an jefa barkonon tsohuwa cikin harabar makarantar, kuma malaman sun yi gaggawar kwashe daliban zuwa wuri mafi aminci.

Tarzomar ta garin Abeokuta tayi salwantar mutuwar mutum guda, wanda bidiyonsa yayi ta kareɗe shafin sada zumunta inda aka ganshi an harve shi da bindiga ya riqe wajen a gefen cikinsa a lokacin da yake qoqarin tsallaka kwata amma ya faɗa cikinta.

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like