Yadda aka yi bikin al’adu na ABUSRC a ABU Zariya
Daga Idris Umar, Zariya
Majalisar Wakilan Ɗalibai ta Jami’ar Ahmadu Bello (ABUSRC) ta fara bikin al’adunta, inda aka fara da gasar girke-girke tsakanin ɗalibai daga jihohi da kabilu daban-daban.
An gudanar da bikin ne ƙarƙashin taken “Haɗin Kai a Cikin Bambance-bambance: Bikin Gadonmu, Ƙarfafa Makomarmu.”
Bikin na kwanaki huɗu ya haɗa ɗalibai da ke wakiltar jihohi da suka haɗa da Adamawa, Bauchi, Imo, Edo, Nasarawa, Kwara, Jigawa, Borno, Akwa Ibom, Plateau da sauran jihohi.
Ku kuma karanta: Cikin Ruwan Sama, Islamiyyoyi sama da 700 ne suka fito zagayen Mauludin Annabi (SAWW) a Potiskum
Dalibai sun baje kolin abincin gargajiya da hanyoyin girke-girke na al’adunsu, yayin da kwamitin alkalai, ciki har da mai ƙirƙirar abubuwan da suka shafi abinci, Chef Amor Hadiza Ango, suka tantance gasar.
Shugaban ABUSRC, Comrade Abdurrahman Halliru Saraki, ya ce an shirya bikin ne domin haɓaka haɗin kai, zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin ɗalibai.


Ya ce shirin yana kuma bai wa ɗalibai damar haɓaka ƙwarewar kasuwanci, lashe kyaututtukan kuɗi da kuma koyon al’adun da suka bambanta da nasu.
Saraki ya ƙara da cewa masu shirya bikin suna ba da kulawa ta musamman ga ƙananan al’adu da kuma ɗaliban da ke da buƙatu na musamman, tare da samar musu da tallafin da ya dace domin su samu damar shiga cikin shirin.
Ya bayyana fatan cewa bikin zai samu karɓuwa har ya kai matakin samun suna a ƙasa baki ɗaya da kuma duniya.
Shirin zai ci gaba a ranar Juma’a da bikin baje kolin kasuwanci, yayin da babban bikin al’adu zai gudana a ranar Asabar.
Mahalarta bikin sun yaba da wannan shiri, inda suka bayyana shi a matsayin wata dama ta musayar al’adu, ƙulla abota da ƙara fahimtar juna tsakanin ɗalibai daga sassa daban-daban na Najeriya.


