Cikin Ruwan Sama, Islamiyyoyi sama da 700 ne suka fito zagayen Mauludin Annabi Muhammad (SAWW) a Potiskum
Cikin mamakon ruwan sama kamar da bakin ƙwarya, ɗaruruwan al’ummar musulmi haɗe da makarantun Islamiyyoyi sama da 700 ne suka fito zagayen Mauludin fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAWW) a garin Potiskum jihar Yobe.
Shi dai irin wannan zagayen Mauludin ana gudanar da shi ne a kowace Asabar ɗin farko na watan Rabi’ul Awwal na kowace shekara.



Makarantun Islamiyyoyi suna taruwa ne a ƙofar fadar mai martaba Sarkin Fika da ke Potiskum, daga nan sai a shiga sahu cikin tsari ana zagaye cikin gari, yayin da Sarkin ke zaune yana kallon masu wucewa.
A lokacin zagayen Mauludin, ana zagaye kusan dukkan manyan titunan cikin garin Potiskum. Garin Potiskum ya tsaya cak, saboda cincirindon masu zagayen Mauludin.
Ku kuma karanta: ‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari’a da sakamako mafi daraja
Ɗaliban Fudiyya da Harisawa suna tafe cikin sahu suna taka faretin girmamawa ga Manzon Allah (SAWW), yayin da ɗimbim al’umma suka yi cincirindon suna kallon su.
A cikin masu zagayen Mauludin na Annabi Muhammad (SAWW), akwai waɗanda suka yi shigar wasu daga cikin ƙabilun ƙasar nan;
- Ibo
- Yoruba
- Kanuri
- Fulani
- Bolawa
- Ngizim
- Kare-Kare
Da sauransu.


