An yi jana’izar ‘yan Shi’a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba’een a Abuja
‘Yan’uwa Musulmi, Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), sun gudanar da jana’izar ‘yan’uwa biyar a muhallin Darur Rahma dake garin Zariya ranar Laraba, 21 ga Safar, 1448AH, daidai da 5 ga Agusta, 2026. Waɗannan mutane sun rasa rayukansu ne sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da su yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Tattakin Arba’een na Imam Husaini (A.S) na shekarar 1448AH/2026 a Abuja.


Wakilin ‘yan’uwa Musulmi, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na Da’irar Zariya da Kewaye, Sheikh Abdulhameed Bello, ne ya jagoranci sallar jana’izar. Bayan kammala sallar, Hurras sun gudanar da faretin girmamawa gare su.
Daga nan aka zagaya da gawarwakin zuwa Mashhadin Shuhada’u na Harkatul Islamiyya tare da faretin girmamawa, kafin daga bisani a bizne su a maƙabartar shahidan Harkar Musulunci da ke Dambo, Zariya.


‘Yan’uwan sun taso ne daga garin Udawa, wani gari da ke maƙwabtaka da Birnin Gwari a Jihar Kaduna. Hatsarin ya faru ne a daren Lahadi, 2 ga Agusta, 2026, a wani gadar ruwa da ke garin Azara, kusa da shiga Jere.
Ku kuma karanta: Miliyoyin ‘Yan’uwa Musulmi A Nijeriya Sun Fara Tattakin Arba’een Domin Tunawa da Imam Husaini (AS)
A nan take mutum guda ya rasu, yayin da ruwa ya kwashe sauran. Bayan kwana biyu na ci gaba da gudanar da bincike a cikin ruwa, an yi nasarar gano gawarwakinsu. Har ya zuwa yanzu akwai mutum 5 da su kuma suka jikkata suna karɓar magani.
Al’amarin ya faru a daidai wata Gada ruwa, da ke gab da shiga garin Jere, bayan faɗawar motan cikin ruwa mutane 4 an samu nasarar ceto su ruwan nan take, da gangar jikin mutum ɗaya ya rasu, sauran 4 ruwa ya tafi da su. Bayan kwana biyu da aukuwar lamarin an yi nasara gano gawarwakin sauran mutun 4 inda aka yi masu Jana’iza.



Waɗanda wannan lamarin ya shafa sun hada da Hussaini M Nuhu Udawa da Abdullahi Mahmud Udawa da Aliyu Muhammad (Monitor) Uduwa da Adamu Abdullahi Uduwa da kuma Mubarak Umar Udawa.


