Online bahislerde yeniliğin ve kazancın buluşma noktası bettilt olmuştur.

HomeFasahaFaransa ta dakatar...

Faransa ta dakatar da aiki a tashoshin nukiliya uku saboda tsananin zafi

Faransa ta dakatar da aiki a tashoshin nukiliya uku saboda tsananin zafi

Gwamnatin Faransa ta dakatar da aikin tashoshin samar da wutar lantarki na nukiliya guda uku, tare da rage yawan wutar da wasu takwas ke samarwa sakamakon tsananin zafin da ƙasar ke fama da shi.

Kamfanin samar da wutar lantarki na EDF ya ce an ɗauki matakin ne domin bin dokokin kare muhalli, waɗanda suka haramta sakin ruwan da ya yi zafi daga tashoshin nukiliya zuwa koguna da tuni zafinsu ya ƙaru saboda yanayin zafi.

Ma’aikatar tattalin arzikin Faransa ta kuma ba da izinin wucin gadi ga tashar Bugey ta ci gaba da sakin ruwan sanyaya zuwa kogin Rhone har zuwa 20 ga Yuli domin tabbatar da dorewar samar da wutar lantarki.

Wannan ne karo na biyu cikin ‘yan makonnin nan da Faransa ke rage samar da wutar nukiliya saboda tsananin zafi. A halin yanzu ƙasar na fuskantar guguwar zafi ta uku tun watan Mayu, inda sama da mutane miliyan 25 suka shiga cikin yanayin da ake hasashen zafin zai kai digiri 41 na Celsius.

Tsananin zafin ya janyo rufe wasu wuraren yawon buɗe ido da wuri, tare da ƙara haɗarin gobarar daji da mace-macen nutsewa a sassa daban-daban na ƙasar.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

‘Yansanda a Katsina sun kama magidancin da ya kashe ‘yarsa, don ta ƙi amincewa da mijin da ya zaɓa mata

'Yansanda a Katsina sun kama magidancin da ya kashe 'yarsa, don ta ƙi amincewa da mijin da ya zaɓa mata Rundunar 'yan sandan ta bayyana mutumin a matsayin Kabir Sani mazaunin unguwar rukunin gidajen 'Shagari Low-Cost'. 'Yansandan sun ce maƙwabtan Kabir...

Kotu a Kano ta yanke wa Amarya hukuncin kisa kan kashe Angonta bayan kwana 9 da aure

Kotu a Kano ta yanke wa Amarya hukuncin kisa kan kashe Angonta bayan kwana 9 da aure Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller Road, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Maryam Sabo, ta yanke wa Saudat Idris hukuncin kisa...

‘Yan bindiga sun sace alƙalin babbar kotun jihar Kebbi

'Yan bindiga sun sace alƙalin babbar kotun jihar Kebbi Rahotanni daga jihar Kebbi da ke Arewa maso Yammacin Najeriya na cewa, 'yan bindiga sun sun yi garkuwa alƙalin babbar kotun jihar Kebbi, Mai Shari'a Faruƙu Hassan Bunza. Wani mazaunin jihar Kebbi,...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.