Online bahislerde yeniliğin ve kazancın buluşma noktası bettilt olmuştur.

Adres güncellemeleriyle sorunsuz bağlantı sağlayan bettilt önemlidir.

Dijital ortamda eğlencenin en güvenilir adresi bettilt oluyor.

HomeGwamnatiKatin shedar ɗan...

Katin shedar ɗan ƙasa ya fallasa kwamandojin Boko Haram 7 da suka dawo daga aikin Hajji – Minista

Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana cewa tsarin tantance bayanan ’yan ƙasa na Hukumar NIMC ya taimaka wajen cafke wasu mutane bakwai da ake zargin manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP ne yayin da suke dawowa daga aikin Hajjin 2026.

Jaridar Punch ta rawaito ministan ya bayyana hakan ne a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan dokar NIMC ta 2026.

A cewarsa, an kama mutanen ne a filin jirgin saman Katsina a ranar Alhamis bayan sun dawo daga Makka, sannan aka miƙa su ga Hukumar Tsaro ta DSS domin ci gaba da bincike.

Ku kuma karanta: Kotu ta soke rajistar jam’iyyar NDC

Tunji-Ojo ya ce an samu nasarar kama waɗanda ake zargin ne saboda haɗa bayanan NIMC da na Hukumar Shige da Fice ta Najeriya tare da alaƙarsu da tsarin bayanan Interpol.

Ya bayyana cewa sabuwar dokar NIMC za ta ƙarfafa tsaron ƙasa ta hanyar haɗa bayanan hukumomi daban-daban, tare da taimakawa wajen yaƙi da ta’addanci, satar bayanai da sauran laifukan tsaro.

Ministan ya ƙara da cewa a baya tsarin bayanan ’yan ƙasa a Najeriya ya kasance a rarrabe, amma yanzu ba za a iya samun fasfo na Najeriya ba tare da amfani da bayanan NIMC ba.

Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan dokar NIMC ta 2026 a gaban shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da wasu manyan jami’an gwamnati.

Get notified whenever we post something new!

spot_img

Create a website from scratch

Just drag and drop elements in a page to get started with Newspaper Theme.

Continue reading

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan wasan Barkwanci, Sani Tumbeleƙe rasuwa

Allah Ya yiwa fitaccen ɗan wasan Barkwanci, Sani Tumbeleƙe rasuwa Rahotanni daga Asibitin Koyarwa na Barau Dikko da ke Kaduna, ya bayyana cewa fitaccen wasan Barkwanci nan Sani Gwarzo Tumbeleƙe rasuwa. Ku kuma karanta: ‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta...

‘Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari’a da sakamako mafi daraja

'Yar shekaru 24, ta zama ɗaliba ta farko da ta kammala karatun Digiri a fannin Shari'a da sakamako mafi daraja Wata matashiya mai shekaru 24, Aisha Widad Yahaya, wadda ita ce uwa ga yaro ɗaya kuma matar aure, ta kafa...

An yi jana’izar ‘yan Shi’a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba’een a Abuja

An yi jana'izar 'yan Shi'a 5 da suka rasu a hatsarin mota a hanyar Tattakin Arba'een a Abuja 'Yan'uwa Musulmi, Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), sun gudanar da jana'izar 'yan'uwa biyar a muhallin Darur Rahma dake garin Zariya ranar Laraba,...

Enjoy exclusive access to all of our content

Get an online subscription and you can unlock any article you come across.