Gasa
‘Yar Gombe mai shekaru 14 ta kafa tarihi a fannin lissafi
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/11/9E210822-7B89-46F9-B37C-CBEA82176DB2.jpeg)
Yarinyar, yar jihar Gombe mai shekaru 14 ta kafa tarihi bayan ta sami lambar yabo ta ƙasar waje har guda 7 a fannin lissafi.
kwararriyar ilimin lissafi, Fatima Adamu Maiƙusa, daga jihar Gombe, ta lashe lambobin yabo na lissafi har guda bakwai.
Fatima na karatu ne a makarantar Nigerian Turkish International (NTIC) da ke jihar Kano.
Ta samu lambobin yabo na ƙasa da ƙasa guda bakwai a fannin lissafi a faɗin duniya da suka haɗa da gasar Lissafi ta Amurka (AMC 08), da gasar Ilmi ta Duniya a Jakarta babban birnin Indonesiya, sai gasar ƙalubalen Lissafi na Duniya a birnin Bangkok na ƙasar Thailand, da sai gasar lissafi ga Kangourou Sans Frontiers (KSF) da kuma gasar lissafi ta Future Intelligence Students Olympiad (FISO), sai gasar lissafi babu iyaka a kasar Bulgaria, da gasar lissafi ta Komodo a kasar Indonesia.
Gasa
Babu rashin jituwa tsakanina da Salah – Klopp
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/05/IMG_8232.jpeg)
A makon da ya gabata ne Salah da Klopp suka yi musayar kalamai a gaban jama’a a wasan da Liverpool ta buga da West Ham wanda aka tashi da ci 2-2.
Kocin Liverpool Jurgen Klop ya dage da cewa babu wata ’yar tsama tsakaninsa da Mohamed Salah saboda an riga an sasanta lamarin.
Klopp ya ce tsawon lokacin da suka kwashe suna mu’amulla da ɗan wasan ɗan asalin ƙasar Masar ya sa dangantakarsu ba ta shafu ba duk da ‘yar tangarɗar da aka samu.
KU KUMA KARANTA:Ronaldo ya ce yana sa ran cin ƙarin ƙwallaye a 2023
A makon da ya gabata Salah da Klopp suka yi musayar kalamai a gaban jama’a a wasan da Liverpool ta buga da West Ham wanda aka tashi da ci 2-2.
Bayan an kammala wasan, da aka tambayi Salah me ya faru, sai aka ji yana cewa, “ idan na yi magana za a yi tashin hankali yau.”
Klopp dai ya ce batun “ba wani abu ba ne” kuma “babu wata damuwa” a tsakaninsu.
Addini
Kano da Bauchi sun lashe gasar Alƙur’ani ta ƙasa ta 2023
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/12/Screenshot_20231231-094501_1.jpg)
Malama Zainab Aliyu Muhammad daga jihar Kano ta zama gwarzuwar gasar Alƙur’ani ta ƙssa ta shekarar 2023 a ɓangaren mata a hadda da tafsiri.
A ɓangaren maza kuwa, Alaramma Ibrahim Muhammad Nasir daga Jihar Bauchi ne ya zama gwarzon shekara a musabaƙar karo na 38, wadda aka kammala a Jihar Yobe.
Mai Masaukin Baki, Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya karamma Malama Zainab Aliyu Muhammad daga Jihar Kano da kyautar mota ƙirar Honda Accord.
Alaramma Ibrahim Muhammad Nasir kuma gwamnan ya gwangwaje shi da kyautar mota ƙirar Honda Accord.
Sannan ya ba da kyautar bas mai ɗaukar mutum 18 ƙirar Toyota Hummer ga Kwamitin shiryar musabaƙa na ƙasa don ci gaba da ɗawainiyar gasar Alƙu’rani.
KU KUMA KARANTA: Yadda aka fara gasar Alƙur’ani ta ƙasa karo na 38 a Yobe
A ranar Asabar ɗin nan aka kammala gasar karatun Alƙur’anin ta ƙasa karo na 38 a Damaturu, fadar Jihar Yobe inda alarammomi daga sassan Najeriya suka nuna bajintarsu.
A lokacin rufe gasar, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar, ya yaba wa matasan da suka shiga wannan gasar ta Karatun Alƙur’ani Mai Girma rukuni-rukuni, sannan ya yi musu fatan alheri.
Sarkin Musulmi, wanda shi ne ya jagoranci taron, ya nuna farin cikinsa bisa yadda aka gudanar da gasar a Yobe cikin kwanciyar hankali kuma a bisa tsari ba tare da an samu cikas ba.
Shi ma Shugaban Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Lawan Sulaiman Bilbis ya yaba wa gwamna Mai Mala Buni bisa yadda ya ɗauki nauyin gasar da kuma yadda aka gudanar da ita cikin nasara.
Cibiyar Nazarin Addinin Musulunci na Jami’ar Danfodiyo ne dai ke shirya Gasar Alƙur’ani ta Ƙasa a Najeriya, kuma wanan shi ne karo na 38.
Mahalarta bikin rufe gasar ta Alƙur’ani sun haɗa da Gwamna Jihar Gombe, Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya, Mataimakin Gwamna Jihar Borno, Mataimakin Gwamnan Jihar Taraba.
Sai masu girma sarakunan Jihar Yobe gaba ɗaya, ƙarƙashin Mai Martaba Sarkin Fika, sai Mai Martaba Shehun Dikwa da ya wakilci Mai girma Shehun Borno, sai Mai girma Sarkin Bauchi da sauran manya-manyan baƙi.
Gasa
Za a gudanar da gasar tseren raƙuma mafi girma a Saudiyya
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230611-WA0001.jpg)
Hukumar da ke shirya gasar tseren raƙuma ta Saudiyya ta ce gasar tseren raƙuma da za a gudanar a wannan shakera a ƙasar za ta kasance mafi girma da aka taɓa yi a tarihin ƙasar.
Hukumar ta fitar da jadawalin gasar da ta ce za a kwashe kwanaki 38 ana gudanarwa.
Jadawalin gasar ya nuna cewa za a fara gasar wadda kusan mutum 600 za su fafata, cikin tsakiyar watan Agusta.
KU KUMA KARANTA: Rundunar Sojojin Najeriya na gudanar da gasar motsa jiki tsakanin sojojin ƙasar
Gasar wadda za a gudanar a birnin Taif ƙarƙashin jagorancin Yarima mai jiran gadon sarautar ƙasar Mohammed bin Salma, an shirya ta ne da nufin nuna muhimmanci da martabar raƙuma a al’adun ƙasar.
An tsara gudanar da gasar ne mataki-mataki, inda za a fara matakin farko na gasar a garin Tabuka, sannan a ƙarƙare gasar a birninTaif.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Dankolo
November 15, 2022 at 7:45 pm
Congrats, wish you many more ahead,god bless you