Connect with us

Laifi

Yadda ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da mutane 53, suka kashe mata masu juna biyu a wasu ƙauyuka huɗu a Neja

Published

on

Wata mata mai juna biyu na wata shida da wasu mutane biyar sun mutu sakamakon harin da ‘yan ta’adda suka kai wa al’ummar Agwa, a ƙaramar hukumar Rafi ta jihar Neja.

Rahotanni sun nuna cewa a yayin harin da aka kai ranar Talata, ‘yan ta’addan, yayin da suke harbe-harbe a cikin al’umma, sun kuma yi garkuwa da mutane 50 zuwa inda ba a san inda suke ba.

Wani ganau mai suna Mallam Audu Muhammad, ya shaida cewa wasu jami’an soji da ke sintiri na yau da kullum a cikin al’umma, sun yi artabu da ‘yan ta’addan, inda ya kara da cewa ‘yan ta’addan sun garzaya dajin domin gudun tsira.

Audu ya ce, “Yan bindigan sun shigo ƙauyenmu ne suka fara harbe-harbe, mutane suka fara gudu don tsira da rayukansu, kuma an kashe kusan mutum shida.

KU KUMA KARANTA: Yan sanda sun kama dattijo da ke yiwa ‘yan ta’adda maganin bindiga

“A yayin da suke harbe harben, sun kuma kama wasu mutane kuma suka yi gaggawar ficewa daga ƙauyen yayin da sojoji suka iso. “Bisa harbin da sojoji suka yi ya fi karfin ‘yan bindigar, don haka sai ,suka gudu zuwa cikin dajin.

Sama da mutane 50 ne aka yi garkuwa da su, wasu kuma sun samu raunuka yayin da suke tsere wa ‘yan bindigar.” In ji shi.

Kwamishinan tsaro na cikin gida da jin kai na jihar, Emmanuel Umar, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce har yanzu ba a tantance ainihin adadin waɗanda abin ya shafa ba.

A wani labarin kuma a ranar larabar da ta gabata, wasu ‘yan bindiga sun sace wasu mutane uku daga al’ummar Beji da ke ƙaramar hukumar Bosso a jihar.

Wani shaidan gani da ido, Abdulahi Aminu, a lokacin da yake zantawa da wakilinmu, ya ce ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar garin ne da misalin ƙarfe ɗaya na safe, inda suka riƙa harbe-harbe.

“Muna cikin barci sai muka fara jin ƙarar harbe-harbe, sai mutane suka fara gudu cikin daji.

‘Yan bindigar sun shiga ƙauyen suna harbin sama da sa’o’i biyu ba tare da tsayawa ba,” in ji Aminu.

Ya ce an kai harin ne bayan babban asibitin Beji ba tare da ‘yan bindigar sun sami wani ƙalubale daga hukumomin tsaro ko ‘yan banga ba.

Aminu ya ce, ‘yan bindigar sun yi awon gaba da wata mata da ‘ya’yanta mata guda biyu waɗanda kuma suka yi awon gaba da wani a kan haya. Amma daga baya ya tsere.”

Ya ce har yanzu ‘yan bindigar ba su tuntubi ‘yan uwa ba domin neman kuɗin fansa, bisa zargin cewa sace su na da alaƙa da gadon wani gidan da aka ajiye da ke cikin unguwar Beji.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 1:30 cikin dare, inda ya ce an aika da wata tawagar dabaru domin ceto waɗanda lamarin ya shafa.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Yadda ‘yan sanda suka ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Zamfara | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa Libya | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa Libya - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Laifi

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Published

on

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Wani matashi ya kashe mahaifinsa a Delta

Ana zargin wani matashi mai suna Ufuoama Umurie ya kashe mahaifinsa a Unguwar Okpare da ke Ƙaramar Hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta, ranar Laraba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, an tsinci gawar mahaifin mai suna Rabaran Isaac Umurie, wanda ɗaya ne daga cikin limaman cocin St. John’s Anglican da ke Okpare-Olomu a safiyar wannan Larabar.

Bayanai sun ce tun farko lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar dare, inda wanda ake zargin ya kori mahaifiyarsa a lokacin da take ƙoƙarin ceto rayuwar mijinta amma ita kanta da ƙyar ta tsira.

Ufuoma, wanda a halin yanzu yana hannun ‘yan sanda, an ce ya yi amfani da laujen yankar ciyawa ya yanka mahaifinsa sannan ya sassare shi a sassan jikinsa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni sun ce matashin ya yi wa mahaifinsa wannan aika-aikar ce a lokacin da yake barci kafin maƙwabta da mabiya cocin su su kawo ɗauki.

Duk da cewa har yanzu ba a gano abin da ya haddasa faruwar lamarin ba, wasu mazauna unguwar yankin sun yi zargin cewa Ufuoma yana fama da taɓin hankali, kuma wannan ne karo na biyu da ya kai wa mahaifin nasa hari.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

Laifi

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Published

on

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Wani mai sayar da maganin gargajiya ya gurfana a gaban kotu bisa zarginsa da yi wa ɗiyarsa mai shekaru takwas fyaɗe.

An gurfanar da magidancin mai shekaru 35 a kan tuhume-tuhume guda na fyaɗe, wanda rundunar ‘yan sandan ta ce ya saba wa sashe na 25 (a) na dokar cin zarafin jama’a ta jihar Ondo ta shekarar 2021.

Dan sanda mai shigar da ƙara, Sufeto Martins Olowofeso, ya shaida wa kotun cewa an kama wanda ake ƙara ne a ranar 18 ga watan Yuni, 2024 bayan rahoton da aka kai ga sashin yaki da garkuwa da mutane na ’yan sanda a Alagbaka, cewa ya yi wa ’yarsa fyaɗe.

Daga bisani an tsare wanda ake tuhuma don ci gaba da bincike.

A cewar Mista Olowofeso, wanda ake zargin tare da matarsa ​​sun gudu daga gidansu bayan aikata laifin inda suka je Jihar Osun suka samo rahoton likita na ƙarya, da ke nuna babu wani abu da ya samu yarinyar.

Ya kuma shaida wa kotun cewa jami’in bincike na ’yan sanda ya sake yin wani gwaji a Akure, wanda ya nuna cewa an zakke wa yarinyar, kuma ta kwashe kwanaki uku tana zubar da jini.

A cewar Olowofeso, wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake zargin sa da shi a lokacin da jami’in da ke binciken ya yi amsa tambayoyi.

KU KUMA KARANTA: An ɗaure ɗan shekara 17 shekaru 14 a kurkuku saboda fyaɗe

Olowofeso ya buƙaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake ƙara a gidan gyaran hali na Olokuta har zuwa lokacin da za ta samu da shawara daga sashen shigar da kara na gwamnati (DPP).

Lauyan wanda ake ƙara, G.O Omoedu, ya shaida wa kotun cewa an kai wa wanda yake karewa sammaci ƙurarren lokaci kuma zai buƙaci lokaci domin ya mayar da martani kan batun shari’a.

Ya buƙaci kotun da ta dage ci gaba da shari’ar don ba shi damar amsa buƙatar ci gaba da sauraren ƙarar.

Majistare B.A. Alipohul ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake ƙara a hannun ’yan sanda sannan ya dage shari’ar zuwa ranar 4 ga watan Yulin 2024.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like