Connect with us

'Yansanda

Yadda ’yan sanda suka kama Murja ‘yar tiktok a Otal

Published

on

Jami’an ‘yan sanda sun kama fitacciyar jaruma a dandalin tiktok mai suna Murja Kunya a otal ɗin Tahir da ke Kano.

‘Yan sandan sun kama ta ne a lokacin da take ƙoƙarin kamawa baƙinta da suka zo daga nesa da kusa ɗakuna domin bikin zagayowar ranar haihuwarta da aketa yaɗawa.

Idan mai karatu zai tuna, Neptune Hausa ta rawaito a watan Satumban shekarar da ta gabata cewa wata kotun shari’a ta rubutawa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano da ya kama Murja Kunya tare da wasu ‘yan TikTok da ake zargi da lalata tarbiyar al’umma.

KU KUMA KARANTA:Muna neman Safara da Mr 442 ruwa a jallo- Afakallahu

Sauran ‘yan TikTok ɗin da ke cikin wasikar sun haɗa da Mr 442, Safara’u, Ɗan Maraya, Amude Booth, Kawu Ɗan Sarki, Ado Gwanja, Ummi Shakira, Samha Inuwa da Babiana.

“Sakamakon ƙarar da Muhd ​​Ali Hamza Esq, Abba Mahmud, Esq, Sunusi I. Umar Esq, Abba, A.T Bebeji Esq, B. I Usman Esq, Muhd ​​Nasir Esq, L.T Dayi Esq, G.A Badawi da Badamasi Suleiman Gandu Esq suka gabatar, Alƙalin kotun mai shari’a ya bada umarni a Bichi reshen Kano don rubutawa tare da roƙon ku da ku binciki waɗanda ake zargin don ɗaukar matakin da ya dace,” daga wani ɓangare na wasiƙar.

Har ila yau, Neptune Hausa ta kuma kawo rahoton cewa an kama Mista 442 a watan Nuwamban 2022 a Jamhuriyar Nijar a lokacin da yake ƙoƙarin samun Visa zuwa Dubai ta hanyar amfani da takardun bogi na ƙasar.

KU KUMA KARANTA:Yadda aka kama Mr 442 da abokinsa da takardun bogi a Nijar

A watan Nuwamban shekarar da ta gabata ne wata kotun majistare ta jihar Kano ta yanke wa wasu matasa biyu Mubarak Isa da Nazifi Bala hukuncin bulala 20 na ranka da kuma yi wa al’umma hidima na tsawon kwanaki 30 bisa samun su da laifin yin wasan barkwanci na TikTok kan gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje.

An yanke wa waɗanda ake tuhumar hukuncin ne bisa tuhume-tuhume biyu da suka shafi ɓata suna da kuma tada hankalin jama’a.

Babban Alkalin Kotun, Aminu Gabari, ya yanke wa mutanen biyu hukuncin bulala 20 na sanda da kuma yi wa al’umma hidima na tsawon kwanaki 30, ciki har da shara da wanke-wanke na harabar kotun da ke Noman’s Land.

Mai shari’a Gabari ya kuma umarci waɗanda aka yanke wa hukuncin da su biya tarar Naira 20,000 ko wannensu, da yin bidiyo a shafukan sada zumunta su nemi gafarar Gwamna Ganduje.

KU KUMA KARANTA: <strong>Kotu ta yanke wa su Mubarak Pikin hukuncin bulala ashirin</strong>

‘Yan sandan a Kano sun Kama Murya Kunya ne a lokacin da take tsaka da shirye shiryen bikin zagayowar ranar haihuwarta, suka ce an sami wani manyyan mutane a Kano da suke ta ƙoƙarin ganin an sake ta

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: &#8216;Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa&#8217;ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like