Connect with us

Boko Haram

Yadda ‘Yan bindiga da ‘Yan Boko Haram suka gwabza a Kaduna

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da suka kai kimanin ɗari biyu a kan babura ɗauke da nagartattun muggan makamai sun kai hari a garin Damari da ke unguwar Kazage da ke Gabashin Ƙaramar Hukumar Birnin-Gwari a Jihar Kaduna.

Bayanai sun nuna cewa an kai harin ne da misalin ƙarfe 5:00 na yammacin ranar Laraba 13 ga watan Yuli yayin da ‘yan ƙungiyar Ansaru wato Boko Haram ke cikin garin suna wa’azi ga mutanen yankin. Da jin ƙarar harbe-harbe daga ‘yan bindigar, ‘yan kungiyar Ansaru suka matsa wajensu suka fara musayar wuta.

A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar masu ci gaba da masarautar Birnin-Gwari, Ishaq Usman Kasai ya fitar a ranar Juma’a, ya tabbatar da faruwar lamarin.

‘’Sun shafe kusan sa’a guda suna arangama sannan ‘yan kungiyar ta Ansaru wadanda suma dauke suke da muggan makamai suka yi galaba a kan ‘yan bindigar wanda hakan ya sa suka ja da baya suka gudu,” inji sanarwar.

A yayin arangamar an yi barna a garin, inda aka ƙona shago, motoci biyu, da wani asibiti mai zaman kansa. An kuma bayyana cewa, ‘yan bindigar sun kuma kashe wasu mutane biyu (leburori) a kan hanyarsu ta dawowa daga gona yayin da ‘yan bindigan ke guduwa cikin dajin.

‘’Saboda haka, mafi yawan al’ummar yankin sun yaba tare da jinjina wa ‘yan Ansaru kan yadda suka kare garin daga harin da ‘yan bindiga suka kai musu inda suka yi imanin cewa lamarin zai iya yin illa sosai.

Ɗaruruwan mutane ne wanda suka haɗa da mata da yara ne suka yi hijira daga garin sakamakon harin. A cewar sanarwar, harin ya kasance tsararren, wanda aka yi shiri ne mai tsauri, domin ‘yan bindigar sun san cewa ‘yan kungiyar Ansaru sun mamaye garin. Don haka, ‘yan Ansaru suka yi masa tirjiya.

Sai dai babu tabbas kan adadin asarar da aka samu tsakanin ‘yan bindigar da ‘yan kungiyar Ansaru. ‘’Yan kungiyar Ansaru na ci gaba da wa’azi da gudanar da shari’a ga mutanen yankin tare da ba su shawarar da su mallaki makamai don kare kansu daga maƙiya tare da yaƙi da Gwamnati domin tabbatar da abin da suke kira daular Musulunci.

Rundunar ‘yan sandan Kaduna ba ta ce uffan ba kan lamarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Boko Haram

Boko Haram sun kashe manoma 15 a jihar Borno

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan ƙungiyar Boko Haram ne sun kashe aƙalla mutane 15 a hare-haren da suka kai kan wasu ƙauyuka biyu a ƙaramar hukumar Jere ta jihar Borno.

Kamar yadda rahoton Daily Trust ta ruwaito, ‘yan ta’addan sun kai farmaki ƙauyen Ƙofa ne da tsakar dare inda suka fara harbe-harbe ba da daɗewa ba, wanda har zuwa safiyar Juma’a.

An tattaro cewa maharan sun kuma kai hari a ƙauyukan Molai Kura da Molai Gana inda suka yi ta yanka mutane da ba a tantance adadinsu ba.

KU KUMA KARANTA: Yadda ‘yan Boko Haram suka yiwa masunta 29 kisan gilla, suka jikkata 9 a Gamborun Ngala

Lamarin dai ya sa mazauna yankin da dama sun ƙauracewa gidajensu zuwa wani daji da ke kusa.

Wani jigo a ƙungiyar ’yan banga, Bukar Ali-Musty, ya shaida wa jaridar cewa manoman na aikin gonakinsu ne a kusa da Molai, da ke wajen birnin Maiduguri, a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, inda ‘yan tada ƙayar bayan suka kai musu hari suka sare kawunansu.

“Aƙalla gawarwaki 15 ne aka kwashe a safiyar yau, an kai hare-haren ne jiya (Alhamis).

“An sare kan manoma bakwai a lokacin da suke aikin gonakinsu, sannan maharan sun kuma yanka wuya ga wasu fararen hula takwas da ba su da illa a gidajensu,” in ji shi.

Wani memba a ƙungiyar ‘civilian JTF’ da ke cikin tawagar da aka kwashe, ya nuna damuwarsa kan hare-haren, yana mai cewa dole ne duk masu ruwa da tsaki su farka don ganin ba a ci gaba da faruwa ba.

“Abin takaici ne ci gaba idan aka yi la’akari da ci gaban da muka samu a cikin watanni ba tare da an kai wa al’umma hari ba.

“Ina can da safe. Ba zan iya tunanin ganin an yanka ’yan uwana kamar rago ba.

Dukkanin gawarwakin da muka ƙwato an same su ne a cikin kwance cikin jini, kuma ina ganin dukkanmu muna buƙatar mu tashi tsaye domin tunkarar wannan maƙiyin zaman lafiya,” inji majiyar.

Continue Reading

Boko Haram

ISWAP ta kashe mutane uku da jikkata sojoji takwas a Borno

Published

on

Aƙalla ‘yan gudun hijira guda uku ne aka kashe tare kuma da jikkata wasu 13 ciki har da sojoji guda takwas a wasu mabambantan hare-hare da ƙungiyar ISWAP ta kai ƙaramar hukumar Damboa na jihar Borno.

An ruwaito cewa lamarin ya faru ne lokacin da ‘yan gudun hijira guda huɗu da ke zama a sansanin Lowcost a Damboa suka fita domin neman itacen hura wuta lokacin da mayaƙan suka buɗe musu wuta, inda suka kashe uku nan take yayin da sauran mutane kuma suka tsere da raunuka.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tun da farko ISWAP ɗin sun jikkata wasu sojoji da kuma fararen hula yayin wani hari da suka kai yankin Talala a ranar Talata duk a Damboa.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da cewa sojoji sun kashe mayaƙan na ISWAP da dama a wani hari da suka kai musu.
Majiyar ta ce wani jrgin sama na sojoji ya je Damboa a jiya Alhamis, inda ta ɗebo sojoji da suka jikkata zuwa Maiduguri domin yi musu magani.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like