Connect with us

'Yansanda

Yadda mata da miji sukayi garkuwa, tare da kashe mai hotel bayan sun karɓi kuɗin fansa miliyan 15

Published

on

Wata mata mai suna Okereke Olufunmilayo, wacce ita ce manaja a wani kantin sayar da kayan gini, tare da mijinta da ɗan aikinta an kama su da laifin yin garkuwa da daraktan Otal din Rolak da ke Ijebu-Ode a Jihar Ogun, mai suna Otunba Abayomi Ajayi Smith.

A cewar mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda jihar Ogun matar ta aikata wannan aika aika ne tare da taimakon mijinta, Larry Adebayo Adewumi, da kuma yaron ɗakinta da ke taya ta aiki mai suna Adebowale Sanni.

Yace ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ma’aikacin otal ɗin ne a ranar 28 ga Satumba, 2020, da misalin ƙarfe 7:30 na safe a rukunin gidajen na Anifowose da ke yankin Igbeba a Ijebu-Ode.

Bayan da suka sace manajan hotel ɗin sun kuma kashe shi duk da sun karɓi kuɗin fansarsa Naira miliyan goma sha biyar.

Tun a wancan lokaci jami’an ‘yan sanda ba su yi ƙasa a gwiwa ba wajen bankaɗo waɗanda suka yi garkuwar tare da kisan ma’aikacin Otel ɗin.

Abimbola Oyeyemi, ya ƙara da cewa ƙoƙarin da rundunar ‘yan sandan jihar ya haifar da nasara a watan Satumban wannan shekara, inda suka samu labarin masu garkuwar na shirin sace mata da ɗan waɗanda suka kashe tun da farko.

Yayin da rundunar ta fara aikin sa ido kan waɗanda ake zargin, ɗaya daga cikinsu mai suna Adebowale Sanni mai shekaru 55, an gano shi a yankin Ikeji Arakeji a jihar Osun, inda nan take aka kama shi.

Yayin da ake masa tambayoyi, wanda ake zargin ya furta cewa shidai umarni aka bashi na ya bi matar mai suna Olusola Roseline Ajayi, wanda umarnin yazo ne daga Larry Adebayo Adewumi shugaban ƙungiyar, wanda matarsa, Olufunmilayo ma’aikaciyar Otunba Ajayi ce.

Ya kuma ƙara da cewa Larry ne ya bayyana ma sa inda otal ɗin wanda aka kashen yake da sauran kayan kasuwancinsa tare da ba shi umarni cewa idan har suka yi nasarar yin garkuwa da matar da ɗanta to dole ne a kashe su biyu bayan sun karɓi kuɗin fansa domin kada su bar wata alama da za a gano su, kamar yadda suka yi wa mijinta shekaru biyu da suka wuce, kama shin da akayi yasa a ka kai ga kama Olufunmilayo da mijinta.

Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa Larry, ɗan asalin garin Ilesha na jihar Osun, ya taɓa zama ɗan damfara kafin ya shiga sana’ar satar mutane na.

“Hanyar aikin da ya yi shi ne ya nemo wani attajirin da aka kashe, daga nan ne ya haɗa gungun ‘yan kungiyar da ke yi masa aiki, Larry ya samu cikakken bayani game da marigayi Otunba Ajayi ta hannun Olufunmilayo, wadda ita ce manajan marigayin.

“Bincike da ‘yan sanda suka gudanar ya nuna cewa Larry yana da asusu guda biyu na banki, “inda yake ajiyar kuɗaɗen da ya samu ta hanyar aikata laifuka.”

Oyeyemi ya kara da cewa cewa wanda ake zargin yana da asusun bankin Jaiz mai lamba 0010913206, da kuɗi N34,953,455. Haka kuma asusun ajiyar sa na bankin Access yana da kudi N4,576,846.

An kuma gano wata mota ƙirar Toyota Highlander 2014 daga hannunsa.

Da yake yabawa tawagar ‘yan sandanbda suka yin aikin kama wanda ake zargin, kwamishinan ‘yan sandan jihar Ogun, Lanre Bankole ya bayar da umarnin a zakulo sauran ‘yan ƙungiyar tare da gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Masu garkuwa da mutane sun kashe wani ɗan kasuwa bayan karɓar kuɗin fansa | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: ‘Yan bindiga sun nemi kuɗin fansa naira miliyan akan ɗaliban da suka sace a kai har Kogi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like