Connect with us

Jan hankali

Yadda aka kashe mijina Musulmi, mahaddacin AlKur’ani, kan zargin yi wa Annabi ɓatanci’

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Batun ɓatanci ga addini a sassa daban-daban na duniya wani batu ne mai sarƙaƙiya da ke bukatar taka-tsantsan. Addinai da Ƙasashe na da dokokin hukunta ɓatanci ga addini.

A ƙasashen da ke bin tsarin shari’ar Musulunci, an tanadar da hukuncin kisa. A jihohi da dama na arewacin Najeriya ma – inda ake amfani da tsarin na shari’ar musulunci da kuma dokokin Ƙasa a lokaci guda – an tanadi hukuncin kisa ga duk wanda ya yi ɓatanci ga addinin Islama.

To amma wani batu da a baya-bayan nan ke sake janyo cece-ku-ce da tayar da jijioyin wuya shi ne yadda wasu fusatattun mutane kan far wa waɗanda aka zarga da yin ɓatanci ga addinin Islama.

Aƙalla mutane biyu ne aka kashe a yanayi mai sarƙaƙiya a baya-bayan nan. An kashe wata ɗaliba kirista a Sakkwato mai suna Deborah Emmanuel, da kuma wani matashi musulmi mai suna Ahmad Usman a Abuja babban birnin kasar.

BBC ta zanta da iyalan wadanda lamarin ya shafa kan halin da suka shiga – da kuma malaman addinai kan wannan batu.

“Kun cuce ni, kun cuci rayuwata”

Ba mabiya addinin Kirista ne kaɗai fusatattu kan far wa ba dangane da batun ɓatanci ga addini.

Cikin watan Yuni, wasu wadanda suka harzuƙa sun far wa wani matashi Musulmi mai suna Ahmad Usman, suka lakaɗa masa duka, suka kashe shi, kana suka ƙona gawarsa bisa zargin cewa ya yi ɓatanci ga addinin Musulunci.

Lamarin ya faru ne a unguwar Lugbe da ke Abuja babban birnin Najeriya.

Na ziyarci gidansu Ahmad, inda na tarar da ƴan uwa da abokan arziki na cikin jimani – cikinsu har da matarsa Zainab, mai zaman takaba.

Watansu takwas da aure kafin a kashe shi. Tana da juna biyu, tana fatan samun ɗansu na fari kuma na ƙarshe.

Zainab na zub da hawaye, dangi na rarrashinta. Ta musanta zargin da aka yi wa mijin nata, tana mai cewa ƙazafi ne.

Ahmad mai shekaru 30 da haihuwa, ɗan banga ne.

Bayanai sun nuna cewa yayin da Ahmad ke sintiri, sai suka yi jayayya da wani malamin addinin Musulunci kan buƙatar malamin ya kiyaye dokar hana fita da dare.

Daga nan Malamin ya zarge shi da yi wa addinin Musulunci ɓatanci. Washegari kuma fustattun suka kashe Ahmad a kusa da ofishin ƴan bangar. Abokan aikinsa sun ce zaƙaƙurin ma’aikaci ne.

Abokan aikin Ahmed Usman

“Wannan ƙazafi da suka yi masa, shi ne ya fi damuna a zuciya’’ a cewar Zainab.

“A kullum mijina ba shi da wata magana sai dai ka ji ya ce ‘mu yi wa Annabi salati’ kuma shi mutum ne da ya haddace Alkur’ani a kansa.”

Ta haƙiƙance cewa babu yadda mai gidan nata zai yi wa Annabi ɓatanci.

Mai dakin Ahmad ta ce saboda irin yadda take jin zafin wannan “ƙazafi” ba za ta yafe wa wadanda suka kashe mata miji ba – amma ta roki Allah “Ya shiryi masu irin wannan hali’’ na ɗaukar doka a hannu ba tare da hujja ba.

“Sun cuce ni, kuma sun cuci iyayensa’’ in ji matar mai juna biyu. Ta yi imanin jajircewarsa a kan aiki ne ya aka yi masa “sharri” kuma lamarin ya kai ga kashe shi.

Zainab ta ce a marainiya ta taso, iyayenta sun rasu tun tana jaririya.

Tana ɗaukar mijin nata tamkar “uwa da uba” saboda yadda yake kula da ita yana kuma tausaya mata, yana share mata hawaye.

Ta ce wadanda suka kashe shi “sun cuce ni, sun cuci iyayensa” kuma yanzu “ban san yadda rayuwa zata kasance mini ba.’’

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: An kashe mahauci har lahira a Sakkwato saboda zargin ɓatanci ga Manzon Allah (SAW) | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

CBN

Jabun kuɗaɗe sun bazu a gari — CBN

Published

on

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ja hankalin ’yan Najeriya kan jabun takardun kuɗin ƙasar da ke yawo a cikin al’umma a sakamakon raɗe-raɗin da ake yaɗawa na ƙarancin tsabar kuɗi.

Kakakin CBN, Hakama Sidi Ali ta shawarci al’umma da su kasance masu lura ganin cewa masu jabun kuɗaɗe na amfani da su a matsayin kuɗin mota ko a wurin yin cefane da gidajen abinci sauransu.

Sanarwar ta CBN ta ce “Dokar CBN ta tanadi hukucin ɗaurin aƙalla shekaru biyar ga duk wanda ya buga jabun kuɗaɗe.

“CBN na aiki da hukumomin tsaro da na hada-hadar kuɗaɗe wajen ganowa da ƙwace jabun kuɗaɗe da kuma tsare masu buga su.” in ji jami’ar.

Daga nan sai ta umarci bankuna, ’yan canji da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗaɗe da su ɗauki matakan da suka dace wajen ganowa da kuma hana yaɗuwar jabun kuɗaɗe.

Ta ƙara da cewa, “ana ƙira ga jama’a su kai ƙarar duk wanda suka ga yana yin jabun kuɗaɗe ga ofishin yan sanda ko na CBN mafi kusa.

Continue Reading

EFCC

EFCC ta fitar da matakai takwas na kare kai daga masu damfara da katin ATM

Published

on

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zangon ƙasa a Nijeriya, EFCC ta koka kan yadda take yawan samun rahotanni na waɗanda aka cire wa kuɗi daga banki ba tare da saninsu ba kuma akasari ta ATM.

Hukumar ta ce akasarin ƴan damfarar sun fi samun bayanan jama’a ko katin ATM ɗin mutane a wuraren cirar kuɗi na ATM ko kuma masu POS.

EFCC ta yi gargaɗi kan cewa ƴan damfarar suna amfani da katin ATM na bankin mutumin da suke so su yaudara, bayan haka sukan je wurinsa da niyyar taimako idan ya shiga ruɗani a gaban ATM.

Hukumar ta ce ƴan damfarar kan yi sauri su yi wa kwastoman bankin musaya da katinsa bayan su haddace lambobin sirrinsa a lokacin da suke ƙoƙarin taimakonsa, wanda daga baya sai su cire kuɗin da ke asusun ajiyarsa.

Dangane da haka ne hukumar ta fitar da hanyoyi takwas waɗanda take ganin idan jama’a sun bi su za su samu kariya daga masu damfarar:

KU KUMA KARANTA: EFCC za ta gurfanar da sojojin saman Najeriya a kotu kan zargin damfara a intanet

  1. Akwai buƙatar ajiye kati a aminctaccen wuri. Duk lokacin da ka karɓi katinka bayan cire kuɗi, ka tabbata katinka ka karɓa ba wai wanda ke kama da katinka ba.
  2. A rinƙa duba sauran kuɗin da ke asusu (balance) domin dubawa ko an cire kuɗi daga asusu.
  3. Saka ƙararrawa domin lura da duk wani abu da ya shafi asusun ajiya ko katin banki.
  4. Rufe lambobin da ake latsawa a jikin ATM ko POS da hannu a lokacin da ake saka lamobin sirri domin cire kuɗi ko wani amfani.
  5. A rinƙa neman taimako daga jami’an banki, ka da ka yi saurin biyan kuɗi ko cire kuɗi.
  6. A ƙira banki domin toshe katin ATM a duk lokacin da aka lura kati ya maƙale a cikin ATM ko kuma duk lokacin da aka lura da wani lamari wanda yake ba daidai ba.
  7. A tabbata an san lambar da za a iya toshe ATM da ita tare da amfani da ita cikin gaggawa a duk lokacin da aka ɓatar da katin ko aka sace shi.
  8. A latsa lambobin USSD na 966911# da kuma bin matakan da suka biyo baya domin toshe katin ATM nan take.
Continue Reading

Jan hankali

NUJ jihar Yobe, ta nuna rashin jin daɗi da ƙara farashi da masu gidajen mai suka yi

Published

on

Daga Ibraheem EL-TAFSEER

Ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Yobe ta bayyana rashin jin daɗin ta game da halin rashin kishin ƙasa da wasu masu gidajen man fetur da ma’aikata suka yi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe da sauran ƙananan hukumomin jihar, dangane da ƙarancin man fetur da aka samu a yau da kuma ƙaruwar farashin mai ɗin, wanda hakan ya jawo dogon layi a gidajen man.

A wata takarda da ƙungiyar ta fitar, wanda shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Yobe, Kwamared Rajab Mohammed da sakatatensa Alhassan Sule Mamudo suka sa wa hanu, ta bayyana cewa, ƙungiyar ta damu matuƙa da halin da ‘yan jihar ke ciki masu son zaman lafiya.

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin man fetur ya jawo hauhawar farashin mai a Najeriya

Don haka muna ƙira ga hukumomin tsaro, hukumomin gwamnati, hukumomin da abin ya shafa da duk masu ruwa da tsaki da su gaggauta ɗaukar matakan da suka dace don ganin an kawo karshen wannan mummunan yanayi da ke iya lalata tattalin arziƙin al’umma.

Za mu iya kwatanta shi a matsayin zagon ƙasa ga tsarin dimokuraɗiyyar Najeriya. Ƙungiyar za ta ci gaba da sanya ido kan lamarin tare da sanar da ‘yan ƙasar kan duk wani ci gaba mai kyau tare da yin ƙira ga kowa da kowa da su kwantar da hankula domin za a shawo kan lamarin cikin ruwan sanyi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like