Connect with us

Hukumar kare haƙƙin bil adam

Ya lakaɗa wa matarsa duka, a kan ta fita ba da izininsa ba

Published

on

Wani magidanci a jihar Zamfara, ya lakaɗa wa matarsa duka, ya farfasa mata jiki, ya kumbura mata idanu a kan ta fita ba da izininsa ba. Matar mai suna Habiba Mustapha, mai shekaru 27, wadda take unguwar Toka, ta kai kuka wajen ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta ƙasa, a kan a ƙwata mata ‘yancinta.

Ta ce mijin nata, ma’aikacin kotu ne, kuma bai taɓa aure ba, ita ce matarsa ta fari. Amma ita taɓa aure kafin ta aure shi. Kuma watansu tara ne da auren. “Daga saɓa ni ya haɗa mu da shi sai ya hau duka na, amma bai taɓa min irin wannan dukan ba” inji ta.

Habiba ta shaida wa ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta ƙasa, reshen jihar Zamfara cewa “abin da ya haɗa mu shi ne, na ce masa zan fita na kai cajin waya, sai ya yi shiru, idan ya yi shiru alamar na tafi kenan. Sai na tafi na kai cajin a maƙwabta, shi kuma ya fita, ya tafi masallaci. Bayan na dawo daga kai cajin, sai na samu ya rufe ƙofofin ɗakunan. Ina ta tun ƙarfe 5:00 na yamma, har sai 11:00 na dare ya dawo. Da ya dawo, sai ya kwanta a falo, ni kuma na shiga ɗaki na kwanta”.

KU KUMA KARANTA: Yadda za a magance yawan kwanciyar gaban ɗa namiji yayin saduwa da iyali

“Da Asuba sai ya tafi masallaci, bayan ya dawo daga sallah, sai ya doki ƙofar ɗakin da ƙarfi, har sai da labulen ɗakin ya faɗo. Da naga labulen ya faɗo, sai na tashi zan gyara labulen, na ɗauka labulen ne ba ya so. Kawai sai na ji ya hauni da duka. Yana ta duka na har na rasa inda kai na yake. Can sai na farfaɗo, sai na ga maƙwabtanmu sun shigo, sun samu ya maƙure min wuya na, ina numfashi da ƙyar. Da ƙyar suka ƙwace ni a hanunsa. Sai ya ce ya sake ni, saki ɗaya”

“Ni dai ban san laifin da na masa ba, amma shi yana cewa, wai na fita ba da izininsa ba. Kuma ai daman ina fita, musamman idan bai bar min abinci ba. Sai na fita na sayo abinci na ci”.

Yaya aka yi idonki ya yi ja kuma ya kumbura haka?

Dukan idon ya dinga yi da hanunsa, yana caccaka yatsunsa a ciki. Daman ya ce ba zai sake ni ba, sai ya yi illa wadda zan fita da ita.

Ko kin sanar da ‘yan sanda a lokacin da abin ya faru?

Eh akwai maƙwabcinmu Nura, shi ne ya je ya sanar da ‘yan sanda, sai suka taho tare. Sai muka tafi ofishin ‘yan sanda. Bayan mun je ofishin ‘yan sanda, sai ya gaya musu abin da na masa, wai na fita ba da izininsa ba. Sai babban ‘yan sanda ya ce “abin da ta yi maka, bai kai ka yi mata wannan duka ba”. Bayan an tattauna, sai yayana ya zo ya yi belina. Shi kuma a hanun ‘yan sanda ya kwana, sai da safe aka ba da belinsa. An kai ni Asibiti, an ba ni magunguna ina sha. Amma har yanzu jikina duk ciwo yake. Sannan ido na ji nake kamar an watsa min ƙasa a ciki.

“Ina so wannan ƙungiya ta kare haƙƙin ɗan’Adam, ta ƙwata min haƙƙina, na irin cin zarafi da lahanta ni da ya yi da duka. Sannan a ƙwata min kuɗi na a hanunsa, naira dubu 41, wanda na ba shi aro ya kuɗin haya” inji Habiba.

Kwamared Salisu Umar, shi ne shugaban ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta ƙasa (mai zaman kanta) reshen jihar Zamfara. Bayan ya saurari koken Habiba, ya ce “wannan rashin adalci ne, kuma ya aikata hakanne da gangan. Yanzu da a ce wannan ɗin ƙanwarsa ce, ko ‘yarsa aka mata haka ba zai ji dadi ba. Sannan kuma abin mamaki shi ne yadda ‘yan sanda suka kashe ‘case’ ɗin ba tare da ɗaukar mataki a kan mijin ba. Yanzu ka duba waɗannan idanun nata za su iya mutuwa. Lallai ‘case’ ɗin bai mutu ba. Yanzu na kira ‘central Police station’ na ce a buɗe ‘case’, a cika ‘file’ a tura ‘case’ ɗin kotu, don a bi mata haƙƙinta.

“Kuma daga yanzu a shirye muke mu ba ta lauya, saboda muna da lauyoyi masu zaman kansu, ƙarƙashin jagorancin Barista Bello Umar. Chamner ɗinsa a tsaye take wajen ba mu gudumawa a jihar Zamfara. Haka ma chamber ɗin Barista Wali da Barista Safiyanu a shirye suke su ba mu gudumawa kyauta ga wanda aka zalunta”. Inji shi

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hukumar kare haƙƙin bil adam

NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa Libya

Published

on

Hukumar yaƙi da fataucin bil-Adama ta Najeriya ta ce tana gudanar da bincike kan lamarin da ya kai ga safarar wasu mata ‘yan Najeriya 11 daga ƙasar.

An ceto ‘yan matan ne a makwaɓciyar ƙasar Jamhuriyar Nijar lokacin da wata ƙungiyar masu safarar mutane ke niyyar jigilar su zuwa ƙasar Libya.

KU KUMA KARANTA:Yadda ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da mutane 53, suka kashe mata masu juna biyu a wasu ƙauyuka huɗu a Neja

Ƴan matan da suka kasance dukkaninsu matasa, an dawo da su gida Najeriya tare da miƙa su ga hukumar hana fataucin mutane ta kasa NAPTIP reshen Sokoto.

Kwamandan NAPTIP na shiyyar Sokoto, Abubakar Tabra ya shaida wa BBC cewa jami’an hukumar kula da shige da fice ta ƙasa reshen Illela ne suka karɓi ‘yan matan a karshen makon da ya gabata, inda ya ce a yanzu sun soma bincike da nufin kamo waɗanda ake zargi da safarar ƴan matan.

Ya kuma ce ana kuma kokarin bincike don gano ‘yan uwan ƴan matan don sake haɗa su da iyalansu.Bayanan da aka tattara sun nuna cewa waɗanda abin ya rutsa da su sun fito ne daga kudancin Najeriya.

Rahotanni sun ce an sace musu wayoyinsu da kayayyakinsu a cikin dazukan Jamhuriyar Nijar, inda waɗanda suka yi safararsu suka yi watsi da su, kafin jami’an ‘yan sandan Nijar ɗin su kuɓutar da su tare da miƙa su ga jami’an shige da fice na Najeriya da ke kan iyaka.

Continue Reading

Doka

Yadda aka kama Mr 442 da abokinsa da takardun bogi a Nijar

Published

on

Hukumomin ƙasar jamhuriyar Nijar sun ce sun fara bincike kan yadda mawaƙan nan biyu ‘yan Najeriya suka mallaki takardun bogi na ƙasar.

Zuwa yanzu mahukuntan ƙasar Nijar na ci gaba da tsare Mubarak Abdulkareem wanda aka fi sani da 442 da manajansa Orler of Kano a gidan yarin birnin Yamai inda suke zaman jiran kammala bincike kamar yadda babban mai shigar da ƙara na gwamnati ya shaida wa manema labarai.

Babban mai shigar da ƙara a ƙasar ya ce babban laifi ne yin amfani da takardun bogi a jamhuriyar Nijar , ya ƙara da cewa sun bayar da umarni a gudanar da bincike domin gano haƙiƙanin gaskiya game da lamarin.

Ya ce ”Duk wanda aka samu da laifi za mu tasa ƙeyarsa zuwa gaban kotu, ba za mu yadda wasu su riƙa amfani da takardun ƙasarmu ta hanya wadda take ba ta gaskiya ba, kuma nan gaba duk wanda aka kama da irin wannan laifin to ya kuka da kanshi”.

A ɗaya ɓangaren ƙungiyoyi masu yaƙin kare haƙƙin bil adama sun fara kiraye-kirayen a bincika domin gano yadda aka yi mawaƙan suka samo takardun zama ‘yan ƙasar, kasancewar sun samo takardun ne a wasu wuraren kafin su zo wajen da za a yi musu fasfo, tare da kiran a yi musu adalci.

Babban mai shigar da ƙarar ya yi watsi da raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewa ana neman belinsu kan sefa (CFA) ta Nijar miliyan 10, ya ce har yanzu babu wata takarda da ke nuna hakan, kuma a cewar sa idan ma ta zo, to hakan ba zai taɓa tabbata ba sai da amincewarsa ko akasin haka.

Continue Reading

'Yansanda

Yan sanda sun ceto yarinyar da ƙanwar mahaifiyarta ta kulle a Filato

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato ta ceto wata yarinya ‘yar shekara 17 da ƙanwar babarta ta kulle a garin Jos babban birnin jihar.

Kamar yadda kamfanin dullancin labarai na Najeriya wato NAN ya ruwaito, cewa jami’ar hukumar kare haƙƙin bil’adama ta ƙasa (NHRC) a jihar Filato, Grace Pam, ta ce an ceto yarinyar ne a unguwar Rikkos da ke ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

Pam ta ce an kawo yarinyar ne domin ta zauna tare da ƙanwar mahaifiyarta bayan kakarta da ke kula da ita ta fara jinya.

“Hukumar ta samu labari daga wani da yayi ƙorafin da ba a bayyana sunansa ba cewa ’yar uwar ta kulle yarinyar a barandar gidan,” inji ta.

Ta kasance tare da kakarta kafin ta zo gidan innar ta saboda kakar ta yi rashin lafiya kuma ba za ta iya ci gaba da kula da ita ba.

Mai ƙarar ya yi ƙorafin cewa innar ta yi tafiyar kusan mako guda kuma ta bar yarinyar babu abinci.
“Bincike ya nuna cewa lallai yarinyar tana fama da rashin abinci kuma tana da tabo a hannunta, wuyanta, da sauran sassan jikinta.

” Tabon ya samo asali ne daga dukan da ake yi mata ba ƙakƙautawa daga wajen innar.

“An kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda inda aka ɗauki bayanin goggon bayan dawowarta daga tafiyar ta.

“An samar wa yarinyar wurin kwana na wucin gadi har sai ta warke.

“Mun kuma gano cewa yarinyar marainiya ce, ba a taba barin ta fita ba, amma an kulle ta a gida, ba a ba ta abinci ba.

“Ɗaya daga cikin abokan aikinmu ne ya kai ta asibiti don tabbatar da an bata kulawar da ta dace” inji shi.

Shugabar hukumar ta NHCR a jihar Filato ta bayyana damuwarsa kan yadda ake samun yawaitar cin zarafin ƙananan yara, inda ya ƙara da cewa, “a yayin da muke magana, akwai wata yarinya ‘yar shekara tara da ta zo ta zauna da goggonta watanni biyu da suka wuce, da ita ma aka ci zarafinta.

“Dole ne muka kubutar da ita a ranar Alhamis daga hannun innarta; ta yi mata dukan tsiya, amma alhamdulillahi, ba ta samu makanta ba sai dai ta samu rauni a ido”.

Ta ƙara da cewa. “Mun kai ta asibiti a ranar Juma’, ta samu da tabo a jikinta sakamakon duka da aka yi mata.

“Lokacin da ma’aikatanmu suka je wurin, an kulle ta a wani gidan kwano da kwano inda goggon ke ajiye awakinta.

“Yarinyar tana fatan komawa wurin iyayenta.” Inji ta.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like