Tag: Jihar Anambra
-
‘Yan sa kai sun maye gurbin ma’aikatan INEC da suka gaza zuwa aiki, a Anambra
Wasu masu kaɗa kuri’a a Ozubulu da ke ƙaramar hukumar Ekwusigo a Anambra, sun ba da kansu a matsayin jami’an wucin gadi na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, bayan da waɗanda aka aiko suka kasa fitowa aikin zaɓen. Masu aikin sa kai sun maye gurbin ma’aikatan wucin gadin ne domin tabbatar da…
-
Ba Buhari ya kawo talauci ba – Ngige ga Obasanjo
Dokta Chris Ngige, Ministan Kwadago da Aiki, ya caccaki tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo kan yadda ya raina shugaba Muhammadu Buhari a sakonsa ga ‘yan Najeriya na sabuwar shekara. A cewar tsohon gwamnan jihar Anambra, ’yan takarar shugabancin ƙasa huɗu na da cancanta da gogewar da ta dace wajen tafiyar da al’amuran ƙasa. Ya yi…
-
An gano gawarwarkin ma’auratan aka sace watanni biyu bayan an biya N7.5 kuɗin fansarsu
An yi jana’izar wasu ma’aurata da masu garkuwa da su suka kashesu, duk da biyan kuɗin fansa. Mutumin, Mista Emmanuel Chukwuemeka, mai shekaru 36, da matarsa, Mrs Chinwendu Chukwuemeka, mai shekaru 30, wasu da ba a tantance ba ne suka yi garkuwa da su tare da kashe su. An binne su ne a garinsu da…
-
Yadda mutum huɗu suka yi wa Yarinya fyade saboda laifin babanta
Hukumar hana fataucin mutane ta ƙasa reshen jihar Anambra tare da haɗin gwiwar ‘yan banga sun cafke wasu mutane uku da laifin yiwa wata yarinya ‘yar shekara 13 fyade. Mutane huɗu ne ake zargi da hannu a lamarin, amma zuwa yanzu mutum uku aka kai ga kamawa yayin da ake neman na huɗun ruwa a…
-
Hatsarin kwale-kwale ya hallaka mutum 76 a jihar Anambra
A ƙalla utum 76 ne aka bayar da rahoton mutuwarsu bayan afkuwar wani hatsarin kwale-kwale a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya. Kwale-kwalen, wanda ke ɗauke da mutum 80, ya kife ne a ranar Juma’a a yankin Ogbaru da ke jihar Anambran. Mafi yawan waɗanda abin ya rutsa da su mata ne da…
-
Daliba ta haifi ‘yan biyar, iyalin sun nemi taimakon gwamnati
Daga Fatima GIMBA, Abuja Wata ɗalibar shekarar ƙarshe a fannin dazuzzuka a Jami’ar Aikin Gona ta Michael Okpara (MOUAU) ta Jihar Abia, mai suna Oluomachi Nwoye, mai shekaru 24, ta haifi ‘ya’ya biyar (biyar) a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Umuahia. A cewar mahaifiyar Oluomachi, Misis Priscilla Nwojo, an haifi ‘yan matan da…
-
Yan Bindiga sun buɗewa tawagar motocin Sanata Ifeanyi Ubah wuta
Yan Bindiga sun buɗewa tawagar motocin Sanata Ifeanyi Ubah wuta a garin Enugwu-Ukwu dake ƙaramar hukumar Njikoka dake jihar Anambra ranar Lahadi. Majiyoyi sun bayyana cewa ana hasashen kimanin yan sandan shida aka kashe a musayar wutar, rahoton Punch. Wata majiya ta bayyana cewa: “Wasu ɓata gari sun kaiwa Sanata Ifenyi Ubah hari a Enugwu…
-
Wani mutum ya kashe ɗan uwansa a dalilin naira 1500 kudin wutar lantarki, a jihar Anambra
Wani mutum mai suna Peter Orji ya kashe ƙaninsa mai suna Godwin Orji kan kuɗin wutar lantarkin N1500 a Nnewi da ke jihar Anambra. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Tochukwu Ikenga ya tabbatar da faruwar lamarin, kuma ya bayyana cewa rundunar ‘yan sandan Najeriya NPF ta kama Peter Orji da…
-
Wata mata ta kashe mijin ƙawarta bayan ya kama su suna maɗigo a gadon sa
Wata mata da ake zargi ƴar maɗigo ce ta kashe mijin abokiyar ta da wuka a kauyen Onitsha dake karamar hukumar Ontisha ta Kudu a jihar Anambra. Wannan mummunar abu ya auku ranar Talatar makon jiya da misalin karfe 9:20 na dare. Magidancin da aka kashe mai suna Ikechukwu Onuma ma’aikacin kwalejin kiwon lafiya ne…
-
Gwamnatin jihar Anambra ta dakatar da shugaban ƙaramar hukama saboda mutuwar matarsa
Daga Fatima GIMBA, Abuja Gwamnatin jihar Anambra ta dakatar da Mbazulike Iloka, sabon shugaban kwamitin riƙon ƙwarya na ƙaramar hukumar Nnewi ta Arewa (LGA) bisa rasuwar matarsa, Chidiebere, a ranar Lahadi, 7 ga watan Agusta, 2022. An sanar da hakan ne a wata wasika mai kwanan watan Agusta, 11, 2022 kuma kwamishinan ƙananan hukumomi, masarautu…