Dubban mutane ne suka yi zanga-zanga a Colombo a ranar Asabar inda suka buƙaci ya yi murabus bayan shafe watanni ana zanga-zangar.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/07/FB_IMG_1657494997963-768x1024.jpg)
Masu zanga-zangar sun ce za su ci gaba da mamaye gidajen shugaban ƙasa da na firaministan ƙasar Sri Lanka, har sai shugabannin biyu sun yi murabus a hukumance. Shugaba Gotabaya Rajapaksa ya ce zai sauka daga mulki ranar 13 ga watan Yuli, kamar yadda kakakin majalisar ya bayyana a ranar Asabar.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/07/FB_IMG_1657494986961.jpg)
Ana dai zargin shugaban kasar ne da tabarbarewar tattalin arzikin kasar, wanda ya janyo karancin abinci da man fetur da kuma magunguna tsawon watanni.
Sai dai ba a ga shugaban ko kuma waninsa ya yi wata sanarwa da kansa ba. Wasu majiyoyin soji sun shaida wa BBC cewa a halin yanzu yana cikin wani jirgin ruwan sojin ruwa a ruwan kasar Sri Lanka. Majiyoyin sun ce dan uwansa, tsohon Firayim Minista Mahinda Rajapaksa, yana sansanin sojin ruwa a ƙasar.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/07/FB_IMG_1657494977508.jpg)
Shi ma Firayim Minista na yanzu Ranil Wickremesinghe ya ce zai sauka daga mukaminsa biyo bayan zanga-zangar da aka yi ranar Asabar, inda aka ƙona gidansa na ƙashin kansa. Sai dai masu zanga-zangar na ci gaba da nuna shakku kan manufar shugabannin.
Leave a Reply