Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana da jami’an tsaro biyo bayan gargaɗin da manyan ƙasashen duniya suka yi na yiwuwar kai hare-haren ta’addanci ƙasar.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/10/FB_IMG_1667212631512-1024x1024.jpg)
A wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan kafafen yada labarai Malam Garba shehu ya fitar, ya ce a yayin ganawar shugaban ƙasar zai saurari bayanai daga manyan hafsoshin tsaron, tare da ƙara ƙaimi a fannonin da ke buƙatar kulawa.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/10/FB_IMG_1667212621805-1024x1024.jpg)
A kwanakin da suka gabata ne manyan ƙasashe kamar Amurka, da Birtaniya, da Canada suka gargaɗi ƴan kasarsu da su yi taka-tsantsan saboda sun samu bayanan da ke cewa za a kai hare-hare a ƙasar, musamman ma a Abuja, babban birnin ƙasar.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/10/FB_IMG_1667212625032-1024x1024.jpg)
Ƙasar Amurka a nata ɓangaren ta buƙaci ma’aikatan ofishin jakadancin ƙasar a Najeriya su fice daga Abuja.
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2022/10/FB_IMG_1667212616443-1024x1024.jpg)
Leave a Reply