No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sugaban Majalisar Dattawan Najeriya Ahmad Lawan ya sha kaye a ƙarar da ya shigar inda yake ƙalubalantar takarar Bashir Machina.

A ranar Litinin, 28 ga watan Nuwamba, 2022, kotun ɗaukaka ƙara da ke zama a Abuja ta tabbatar da hukuncin da babbar kotun tarayya da ke zama a Damaturu a jihar Yobe ta zartar.

Kotun ta ce Bashir Machina ne ɗan takarar jam’iyyar APC mai wakiltar Yobe ta Arewa a majalisar dattawa ba Ahmad Lawan ba.

Honourable Justice Monica Dongban-Mansen wacce ta jagoranci kwamitin mutum uku ta yanke hukuncin ne a wata ƙara da Ahmad Lawan ya shigar gaban kotun, Lawan ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta Damaturu ta yanke.

A cikin ɗaukaka ƙarar, ya buƙaci kotun ɗaukaka ƙara ta bayyana shi a matsayin halastaccen mai riƙe da tutar jam’iyyar APC a zaɓen sanata mai zuwa. Kotun ta yi watsi da ƙarar saboda rashin cancanta.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...