Ruwan sama na kwana uku ya hana Kanawa fita neman na abinci

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Al’ummar jihar Kano a arewacin Najeriya na ci gaba da bayyano ra’ayoyinsu dangane da yadda aka yi ta mamakon ruwan sama na kwanaki uku a jere.


Ruwan saman ya tsayar da harkokin ciniki da dama a babban birnin jihar. Ba kasafai ba dai ake samun mamakon ruwan sama da za a jera irin wadnan kwanaki har uku ana ruwa ba, da ya wuce awanni ba.


Wannan mamakon ruwan saman da aka samu a jihar ya jefa wasu daga cikin iyali halin ƙunci sakamakon rashin samun damar fita a samo abin kai wa baka saboda ruwan da ake yi.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *