Connect with us

'Yansanda

Masu garkuwa sun sace matasa 21, har da budurwa da ke aikin tara kuɗin aurenta

Published

on

Sace matasa 21 da ‘yan ta’adda suka yi a wata gona da ke kusa da ƙauyen kamfanin Mai ‘Yardua da ke ƙaramar hukumar Faskari a Jihar Katsina a ranar 30 ga Oktoba, 2022, ya jefa mazauna yankin cikin fargaba.

Da yake magana game da sace ‘yan matan, wani mai suna Muntari Auwalu ya ce ‘yar wansa na ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa. Mutumin mai tuƙa babur ne a Katsina, ya ce an kira shi ne a ranar Lahadi da daddare cewa an yi garkuwa da ‘yar wansa mai suna Asiya tare da wasu ‘yan mata a rana tsaka a lokacin da suke a gona.

Ya ce a ranar Laraba ana ƙoƙarin samo hanyoyin neman kuɗin fansa da ‘yan ta’addan ke nema a kan waɗanda suka yi garkuwa da su. Auwalu, wanda bai bayyana adadin kudin ba, ya ce, “da tsakar daren ranar Lahadi aka kira ni cewa an yi garkuwa da Asiya, kuma har yanzu ‘yan ta’addan ba su kai da gaya mana abin da suke bukata ba.

“Asiya tana shirin bikinta. Ina tsammanin hakan ya sa ta je ta yi aikin gona domin ta sami kuɗin bikin, amma aka sace ta. ” Yanzu haka a Katsina na ke zaune ina tuƙa babur na acaɓa ina kuma taɓa kasuwanci tunda ‘yan ta’adda sun hana mu komawa gonakinmu a Mairuwa.”

Ina tuntuɓar gida kowace rana kuma kamar yadda a safiyar jiya Larabar an faɗa mani cewa ‘yan ta’addar sun bayyana buƙatunsu yayin da aka nemi na bayar da nawa gudummawar. “Ba zan iya gaya muku adadin kuɗin ba kasancewar mutanenmu a gida ne suke da gaskiyar ƙididdigar, kira na ga gwamnati da ta inganta tsaro a cikin a yankin.”

Ni da wasu da dama daga ƙauyen Mairuwa muka ƙaura saboda ‘yan ta’addan” inji shi.Mazauna yankin sun ce ‘yan ta’addan sun kewaye gonakin ne da misalin karfe 3 na yammacin ranar Lahadi, 30 ga watan Oktoba, 2022, a lokacin da matasan ke aikin girbin amfanin gona a gona.An ce an ɗauki matasan ne a matsayin leburori daga al’ummomin da ke kewaye da gonar, inda aka ce yawancinsu ‘yan ƙauyen Mairuwa ne.

Jerin sunayen waɗanda abin ya shafa da rundunar ‘yan sandan Katsina ta bayar ya nuna cewa akwai ‘yan mata a ƙalla bakwai a cikinsu. Lissafin ya kuma nuna cewa waɗanda aka kashen ‘yan t shekaru 16 zuwa 21, haka zalika sunayen waɗanda abin ya shafa kamar yadda aka samu daga rundunar ‘yan sandan su ne Lawal, mai shekaru 18, sai Mandiya ‘yar shekara 18 da Bilkisu ita ma mai shekaru 18 sai Samaila ɗan shekara 16 da Awanu shima mai shekaru 16, sai Dalha mai shekaru 21 da kuma Umeh Abdullahi ‘yar shekara 18 da Hadiza mai shekaru 17, sai Ibrahim Dalha mai shekaru 17, da Zainab ‘yar shekara 17 da Aliyu Baba mai shekaru 15 da Yusufu Dana shima mai shekaru 15.Sauran su ne Abdullahi mai shekaru 18, da Samaila, mai shekaru 18, sai Shehu mai shekaru 17, Asiya Abdul mai shekaru 19 sai Zuwaira mai shekaru 16 da Abdullahi mai shekaru 17, Amina ‘yar shekara 18 da Sani ɗan shekara 15 sai Nafiu mai shekaru 17.

Mazauna yankin sun kuma ce mai gonar da aka yi garkuwa da yaran yana zaune ne a Funtuwa kuma yakan ziyarci gonakin ne kawai a wasu lokuta. An kuma yi zargin cewa a baya mai gonar ya bai wa ‘yan ta’addan Naira miliyan ɗaya domin ya girbe amfanin gonarsa ba tare da an yi musu fyade ko kuma sace masu yi masa aiki a gonar ba, sai dai babu wanda zai iya tabbatar da hakan duk da haka.

Haka kuma, wani mutum da aka ce shi ne manajan gonar ba a iya gano shi a ranar Laraba ba. Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma bayyana cewa an yi garkuwa da matasa 21. Ya ce, “An yi garkuwa da matasan ne a ranar 30 ga Satumba, 2022, da rana, amma rahoton faruwar lamarin ya kai ga ‘yan sanda da karfe 7.40 da yamma.”Waɗanda aka yi garkuwa da su 21 ne. Tun daga wannan lokacin, muna ta ƙoƙarin ganin an ceto su, duk lokacin da aka samu sabon ci gaba, zan sanar da ku.”

Bamu samu jin ta bakin mai baiwa gwamna Aminu Masari shawara kan harkokin tsaro ba, Ahmad Katsina domin jin ta bakinsa duk da cewa tuni jihar ta hada kai da jami’an tsaro domin ceto yaran. A halin da ake ciki kuma, a ranar Larabar da ta gabata an samu rahotannin cewa barayin na neman Naira miliyan 30 a matsayin kudin fansa.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Yadda ‘yan sanda suka kama gungun ɓarayin waya a Alaba-rago da Ajegunle a jihar Lagos | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like