Connect with us

Labarai

Majalisar Dattijai za ta cire hukumar kula da Injiniyoyi daga kasafin kuɗi na 2023

Published

on

Majalisar Dattijai ta ce babu gudu babu ja da baya wajen cire hukumar kula da injiniyoyi ta ƙasa COREN daga kasafin kuɗin 2023, tare ƙin ba ta ko Kobo a cikin kasafin kuɗin shekara mai kamawa.

Dambarwar ta soma ne lokacin da kwamitin ayyuka da Sanata Adamu Aliero yake shugabanta ya buƙaci rajistara na hukumar, Ademola Bello, da ya yi bayanin yadda hukumar ta kashe kuɗin da aka ware mata a kasafin kuɗin da ya gabata na wannan shekara ta 2022.

Kamar yadda rajistaran hukumar ya faɗa, an ware wa hukumar biliyan 2.4 a kasafin kuɗin wannan shekara ta 2022 kuma sun kashe biliyan 1.2 wajen shirya babban taron ƙungiyar na ƙasa.

Bello ya ce kuɗin ma’aikata ya ƙaru zuwa miliyan 200 a kasafin bana saboda COREN ta tsara cewa za ta buɗe ofisoshinta a jihohi 36 na ƙasar nan a 2023.

Da yake amsa tambayar shugaban kwamitin, Sanata Adamu Aliero; Bello ya ce COREN ta sanya kuɗi Naira miliyan 45 ga asusun gwamnatin tarayya wanda shugaban kwamitin ya buƙaci su kawo takardar aikewa da kuɗin zuwa asusun gwamnati.

Ɗaya daga cikin mambobin kwamitin, Sanata George Sekibo, ya ce babu dalilin cigaba da sanya hukumar Injiniyoyin a kasafin kuɗin ƙasa duba da yadda gwamnati ba ta amfana da hukumar duk da kuɗin masu yawa da take sakawa kan hukumar a kasafin kuɗi.
Ya ce ta yaya za a ba ku kuɗi har biliyan 2.4 amma kuma ku dawo da miliyan 45 ga asusun gwamnati a matsayin kuɗin shiga?

Ya ce ya kamata COREN ta tsaya da ƙafarta, kamar yadda ƙungiyoyin ƙwararru irin su ƙungiyar lauyoyi da ta likitoci da sauransu suka tsaya da ƙafarsu ba tare da sanya su cikin kasafin kuɗin ƙasa ba.

a ƙarshe dai kwamitin Sanata Adamu Aliero na ayyuka ya buƙaci COREN da su je su kawo takardun da ke nuna suna sanya kuɗaɗe ga asusun tarayya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like