Connect with us

Fyaɗe

Likitan da yayi wa ƙanwar matarsa ‘yar shekara 15 fyaɗe ya ce ba budurwa ba ce inji shaidu

Published

on

Wata ƙwararriyar likitan yara, Misis Olabisi Ajayi-Kayode, a ranar talata, ta shaida wa wata kotun laifukan jima’i ta jihar Legas da ke Ikeja, cewa wata ƙaramar yarinya ‘yar shekara 15 da ake zargin mijin yayarta Dokta Olufemi Olaleye ya lalata ta, ta ce wanda ake ƙara yayi tsokaci akan budurcinta.

Likitar yaran ta bayyana cewa wanda abin ya shafa ta kuma shaida mata cewa wanda ake zargin, Dokta Olaleye,wanda daraktan likitoci ne na gidauniyar kula da cutar kansa, bayan ya yi mata fyade, ya yi amfani da takarda mai laushi wato tissue wajen goge jinin da ke fitowa daga al’aurarta.

Ajayi-Kayode, Lauya da ke aiki da gidauniyar ceceton yara, ta ce a binciken da ta yi, ta gano cewa Olaleye ne ya lalata yarinyar.

Olaleye na fuskantar tuhume-tuhume biyu, na lalata da kuma lalata yarinyar, wacce ‘yar uwar matarsa ce.

KU KUMA KARANTA:Yadda wani mutum yayi wa Yaro fyaɗe har ya mutu

Lauyan wanda Darakta mai gabatar da ƙara na jihar Legas, Dokta Babajide Martins ya jagoranci gabatar da ƙara a gaban kotu, ya ce yarinyar ta shaida mata cewa wanda ake zargin ya fara ne da sanya hannunsa a karkashin rigarta ta bacci tare da taba al’aurarta.

Ta bayyana cewa wanda ake tuhumar yana sata ta tsotsi al’aurarsa, inda ta ƙara da cewa yakan aikata laifin ne a wani sashe na ɗakin zama da kyamarar talabijin mai leƙen asiri bata aiki.

Ajayi-Kayode, wanda ya bayar da shaida a gaban mai shari’a Ramon Oshodi a matsayin mai gabatar da ƙara na uku, ya ce yarinyar ta bayyana cewa wanda ake ƙara ya tambaye ta ko har yanzu budurwar ita budurwa ce?

Ta ce, “Ya ce, ‘ke har yanzu budurwa ce?’ ta ce, ‘eh’ sai ya ce, ‘Me ya sa har yanzu ke budurwa? Babu sauran a cikin salon; ‘yan matan masu shekaru 12, 13, da 14 da suke kasancewa budurwai. “A matsayina na likita, zan iya ɗaukar nauyin ‘yan matan da suka rasa budurcinsu kuma suka sami ciki”

To, shawarar taku ce.’ “Sai ya tambaye ta cewa, ‘Za mu iya zama abokai?’ Kuma ba tare da ja ba, yarinyar ta ce ta amsa cewa, ‘Mun riga mun zama abokai.’

“Mun tambaye ta ko akwai wanda ya taba yi mata haka, sai ta ce a’a. Yarinyar ta ce a karon farko da mijin yayarta ya yi lalata da ita, abin ya yi zafi kuma akwai jini sai ya dauki abu ya goge jinin.

Mai gabatar da shaidan ya ci gaba da cewa, wadda aka yi wa fyaɗe, ta shaida cewa, a wani lokaci, yayarta tana bata umarnin cewa kada ta zauna ita kaɗai a cikin gidan, amma da wanda ake kara ya iso sai ya ce da ita, ta bi shi cikin gida.

Ta ce, “Da suka shiga gidan, sai ya ce ta shirya masa ‘amala’. Ana cikin haka sai ya shigo kicin, ya kai ta wajen karatunsa ya yi lalata da ita, sannan ya gargaɗeta da kada ta faɗawa kowa.

Ta ce abin ya dame ta sai ta fara tunanin ta gaji da abin da likitan ke yi mata, ba tare da sanin direban ya ji ta ba.

Ajayi- Kayode ya ƙara da cewa, “Mijin yayarta, ya daɗe yana lalata da yarinyar, ba sau ɗaya ba, kuma ya yi amfani da barazana, da kuma tilastawa.

“Ya yi amfani da matsayin shi na mijin yayarta, don samun damar saduwa da yarinyar don yin jima’i, kuma barazana da tilastawa sun kasance don kula da yarinyar.

“Ya yi amfani da budurcin yarinyar inda ya gaya mata cewa budurci ba ya wanzuwa kuma”

Bayan bayanin kwararren lauyan mai gabatar da ƙara ya buƙaci kotun da ta amince da sakamakon binciken da shedun ya samu da kuma takardar shaidar.

A yayin da ake yi wa masu gabatar da shedar tambayoyi, lauyan wanda ake ƙara, Babatunde Ogala, SAN, ya yi ƙoƙarin ɓata hujjojin nata, inda ya bayyana cewa ta yanke hukuncin ne a kan mu’amalarta da yarinyar.

Ta amsa da cewa ta kuma yi magana da masanin ilimin halayyar ɗan adam da kuma ‘yan sanda. Lokacin da aka tambaye ta ko ta ga rahoton likita kafin yin magana da wanda aka yi wa fyaɗen? ta amsa, “Ban ga wani rahoton likita ba amma DPP ta gaya mani game da rahoton likita.”

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: ‘Yan bindiga sun harbe ɗan sanda a lokacin da yake saduwa da budurwar sa a daji | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Fyaɗe

Fyaɗe: An ba da belin Dani Alves, tsohon ɗan wasan Brazil kan dala miliyan 1.1

Published

on

Wata kotu a Sifaniya ta ba da belin tsohon ɗan ƙwallon ƙafar Brazil da kuma Barcelona, Dani Alves, kan dala miliyan 1.1.

Sauran sharuɗɗan belin sun haɗa da cewa Alves zai ajiye fasfo ɗinsa na Brazili da na Sifaniya, domin gudun ka da ya fice daga Sifaniyar.

A ranar Laraba ne wata kotun Barcelona ta ce za a iya sakin Dani Alves daga gidan yari kan belin dala miliyan 1.1, yayin da yake aukaka ara kan shari’ar da ake masa kan aikata fyaɗe, bayan ya yi zaman kusan kwatan wa’adin shekaru huɗu na hukunci.

Haka nan kuma, kotun ta ɗora masa dokar hana Alves zuwa kusa da wadda ya aikata laifin kanta, da tazarar mita 1,000.

KU KUMA KARANTA: Ana yi wa yara fyaɗe sakamakon yaƙin da ke faruwa a Sudan – MƊD

An tsare tsohon ɗan wasan baya na Barcelona da Juventus da PSG a wani gidan yari na Barcelona tun watan Janairun 2023.

An yanke wa Alves hukunci ranar 22 ga Fabrairu, kan laifin yi wata mata fyaɗe a banɗaki wani gidan rawa na Barcelona a 2022, kuma aka umarce shi ya biya ta Euro dubu 150,000.

Sai dai ya ɗaukaka ƙara kan hukunci, kasancewar hukuncin ba shi ne na ƙarshe ba.

Continue Reading

Fyaɗe

Wani hedimasta ya yi wa ‘yar shekara shida fyaɗe

Published

on

An kama wani hedimasta a jihar Bauchi da laifin yi wa ‘yar shekara 6 fyaɗe.

Mai shari’a Nana Fatimah Jibrin, shugabar babbar kotun jihar Bauchi mai lamba 11, ta yanke hukuncin ɗaurin shekaru 11 a gidan kaso ga wani Hedimasta a garin Burra da ke ƙaramar hukumar Ningi mai suna Jalaludeen Zakari bisa samunsa da laifin yin lalata da wata yarinya yar shekara 6.

Yarinyar ta kasance a makarantar don yin jarabawar shiga makarantar amma Zakari ya tsare ta tsawon sa’o’i bayan an rufe makarantar a hukumance.

Barista Dayabu Ayuba, lauya mai shigar da ƙara kuma lauyan jiha a ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, wanda ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a ranar Talata, 2 ga watan Janairu, 2023, ya ce wanda ake tuhumar ya shigar da yatsarsa a cikin al’aurar yarinyar.

KU KUMA KARANTA: Shekara 3 bayan ya yi wa ‘yar shekara 4 fyaɗe, kotu ta yanke mishi hukunci

Ayuba ya ce a lokacin da ake shari’ar, shaidu uku ciki har da wanda aka yi wa lalata, sun ba da shaida a gaban kotun.

“Mai laifin ya buƙaci yarinyar da ta tsaya, ya sallami sauran ɗaliban bayan an tashi daga makaranta, ba tare da bayar da dalilin tsawaita zaman yarinyar ba. 

Yayin da aka bar ta a baya, hedimasta ya ya kai mata harin lalata, wanda ya yi daidai da fyaɗe a shari’ance,” inji shi.

Ayuba ya ce an yanke hukuncin ne a watan Yulin wannan shekara bayan Jalaludeen ya roƙi kotu da ta yi masa sassauci.

Continue Reading

Fyaɗe

Kotu a Kebbi ta ɗaure yaron da ya yi wa ƙananan yara biyu fyaɗe

Published

on

Wata babbar kotun majistare da ke zamanta a Birnin kebbi ta samu wani matashi ɗan shekara 16 Habibu Umar da laifin yin lalata da yara ƴan mata kuma aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru uku a gidan gyaran hali.

Ɗan sanda mai gabatar da ƙara Insp.  Muntari Mati, a ranar Alhamis, 23 ga watan Nuwamba, 2023, a wata ƙara mai lamba BK/538C/223,  ya gabatar da Habibu Umar a gaban kotu bisa tuhuma guda ɗaya na cin zarafi ta lalata wanda ya saɓawa sashe na 263 na ƙundin laifuffukan Penal na jihar Kebbi.

Habibu ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi a gaban kotu, Alkalin Kotun Samaila Kakale Mungadi don haka ya yanke wa Habibu hukuncin ɗaurin shekaru uku a gidan yari tare da zaɓin biyan tarar naira dubu ɗari da hamsin (N150,000).

KU KUMA KARANTA: An kama yaro ɗan shekara 16 a Kebbi bayan ya yi wa ƙananan yara 2 fyaɗe

Zaku iya tuna cewa Neptune Hausa ta ruwaito cewa jami’an tsaron Masarautar Gwandu ne suka kama Habibu Umar wanda hakan ya sa aka ƙara ɗaukar mataki.

Bayan an yi masa tambayoyi na farko a Fadar Ubandoman Gwandu, daga baya aka miƙa shi ga hukumar Hisbah ta jihar Kebbi, bayan da aka yi zargin ya lalata wasu ƙananan ‘yan mata biyu masu shekaru biyar da shida a wani daji da ke tsakanin unguwar Badariya da Barikin Sojoji a Birnin kebbi a ranar 21 ga Nuwamba 2023.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like