Connect with us

Doka

Hukumar Hisbah ta kama mata da maza 23 a wuraren da basu daceba a Nasarawa GRA

Published

on

Daga Shafaatu DAUDA, Kano

Dakarun hukumar Hisbah na jihar Kano masu hani ga munanan aiyuka, da kuma yin nuni ga kyakkyawa, a daren jiya ne su ka kai sumame a gidaje 3 da ake zargin samari da yan mata kan hadu su sha shisha da sauran kayan maye, daga bisani su aikata masha’a.

Tun da fari, Babban kwamandan hukumar Hisbah, Dr Harun Muhammad Sani Ibn sina yace maƙwabtan waɗanan gidaje da ake zargi sune suka kaiwa hukumar ƙorafi, a lokuta daban-daban, tare da nuna takaicin yadda ake barin ƙananan yara shiga irin wancan gida.

A lokacin sumamen an sami nasarar cafke matasa 23 maza 4 sai yan mata 19 a lokacin da suke tsaka da busa tabar shisha, inda Dakarun Hisbah ba su yi wata-wata ba su ka damƙo su izuwa shalkwatan hukumar Hisbah.

Binciken da dakarun Hisbah na farin kaya su ka gabatar, ya tabbatar da cewa ana Shan shisha da sauran kayan sa maye, baya ga aikata badaƙala a gidan.

Wuraren da aka damƙo matasan sun hadar da na titin Tukur road a unguwar nasarawa, da na titin sultan road, shi ma a unguwar nasarawa, da Kuma zuwa asibitin Nasarawa wato hospital road.

A cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran hukumar Lawan Ibrahim fagge ya aikowa Neptune prime, yace Babban kwamandan hukumar Hisbah, Dr. Muhammad Sani Ibn Sina ya yi tsokaci, inda ya ba da tababbacin cigaba da kai sumame har ma da ɗaukan matakan shari’a a kan irin waɗannan gidajen.

Sannan ya gargadi iyaye tare da Jan kunnen matasa da su guji jefa kan su cikin aiyukan masha’a domin samun shuwagabanni na gari.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: ‘Ta kashe aurenta don ta auri tsohon saurayin ‘yarta’ | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Doka

Kotu ta umarci jihar Ondo da ta biya diyyar naira miliyan 30 ga mutumin da ‘yan Amotekun suka harbe

Published

on

Ta kama mijinta yana lalata da ’ya’yan cikinsu

Wata babbar kotun Ondo da ke zamanta a Akure, a ranar Larabar da ta gabata ta umarci gwamnatin jihar Ondo da ta biya wani Oluwasegun Oluwarotimi kuɗi naira miliyan 30 a matsayin diyyar harbin bindiga da ya samu a wata arangama da jami’an tsaro na jihar, wanda aka fi sani da ‘yan Amotekun.

Oluwarotimi mai shekaru 36, mai tuƙa babur ne, wato ɗan okada ne lokacin da lamarin ya faru.

A nasa jawabin, Mai shari’a Adejumo ya bayar da umarnin a biya Oluwarotimi kuɗi naira miliyan talatin a matsayin diyya.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NYSC ta biya diyya ga dangin ɗan bautar ƙasa da ya ɓata

Oluwarotimi, wanda a yanzu an yanke shi ne sakamakon harbin da aka yi masa ba bisa ka’ida ba,inda ya shigar da karar a gaban kotu.

“B bisa ka’ida ba a titin Araromi a ranar 9 ga watan Agustan 2021 a Akure, harbin da Amotekun ta yi ya saɓa wa hakkin ɗan Adam.

“Kotu ta umurci waɗanda ake ƙara da su hada kai su biya Naira miliyan 20 ga wanda ake kara a matsayin diyya na gaba daya da kuma Naira miliyan 10 a matsayin diyya ta misali,” in ji alkalin.

Continue Reading

Doka

An sanya dokar hana fita a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sanya dokar ta-ɓaci har zuwa faɗuwar rana don kaucewa taɓarɓarewar doka da oda, biyo bayan tattara sakamakon zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar da safiyar Litinin.

KU KUMA KARANTA: Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya lashe zaɓen Kano

Ya ce an yanke shawarar ne don hana ’yan daba su haifar da hargitsi a halin da ake ciki.

Kwamishinan ya yi kira ga jama’ar jihar da su kasance a cikin gida domin jami’an tsaro ba za su ƙyale kowa ko wata ƙungiyar da ke da niyyar haddasa fitina ba.

Continue Reading

Doka

Kotu ta sanya sharudɗa akan batun bada belin doguwa

Published

on

sharudɗan sune kamar haka:

Kotu ta haramtawa Alhassan Ado Doguwa zuwa mazaɓarsa ranar zaɓen ta gwamna da ‘yan majalisar jiha.

Wannan dai na cikin sharudɗa da babbar kotun tarayya ta sanya kafin bada belin Alhassan Ado Doguwa.

Ga dai ƙarin jerin sharudɗan da kotu ta sanya kafin bada belin.

1- Zai ajiye zunzurutun kuɗi har naira miliyan 500

2- Gabatar da sarki mai daraja ta ɗaya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

KU KUMA KARANTA: INEC ta cire sunan shugaban masu rinjaye, Doguwa daga jerin sunayen ‘yan majalisar wakilai

3- Gabatar da babban sakatare a gwamnatin jiha ko ta tarayya a matsayin wanda zai tsaya mishi.

4- Zai ajiye Fasfo da sauran dukkanin takaddunshi na tafiya a kotu.

A karshe kuma kotu tace bazai halacci mazaɓarsa ba yayin zaɓen gwamna da yan majalisun jiha dake tafe.

Ko ya kuke kallon wannan batu?

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like