Connect with us

Labarai

Gwamnan Kaduna zai ba da ilimi kyauta ga ɗaliban Kuriga

Published

on

Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya yi tayin ba da ilimi kyauta ga ɗaliban makarantar Kuriga da aka kuɓutar a ƙarƙashin gidauniyarsa.
Gwamnan ya kuma sha alwashin sake gina makarantun firamare dana sakandaren Kuriga tare da samawa al’ummar yankin kayayyakin more rayuwa.

A jawabinsa ga ɗaliban gabanin tashinsu zuwa Kuriga a ranar Alhamis, Gwamna Sani ya ba su tabbacin cewar al’amarin yin garkuwa da su ba zai shafin batun ilminsu ba, inda yace an tabbatar da ingantaccen tsaro ga al’ummar garin kuriga domin su ci gaba da rayuwa cikin walwala da aminci.

“Na umarci gidauniyar uba sani wacce ta shafe fiye da shekaru 16 tana ba da ilimi da lafiya kyauta, ta ci gaba da kula dasu.

“Na kuma ba da umarnin a gudanar da gyare-gyare a makarantu da garin Kuriga, domin a wurina Kuriga gari ne me son zaman lafiya a jihar Kaduna”.

Ya kuma sanar da gudunmowar Naira miliyan 10 ga iyalan Shed Mastan, Abubakar Isah da ya mutu a hannun masu garkuwa da mutane, sannan ya yi tayin ɗaukar nauyin karatun ‘ya’yansa har zuwa matakin jami’a.

KU KUMA KARANTA:An saki ɗaliban makarantan Kuriga da aka sace a jihar Kaduna

“Gwamnatin jihar Kaduna za ta ci gaba da tallafawa karatun ‘ya’yan Malam Abubakar. Kuma za mu tallafawa iyalansa da gudunmowar Naira miliyan 10 domin halin da suka tsinci kansu a ciki. Malam Abubakar ya rasu ne sakamakon wata jinya da yake fama da ita. Muna roƙon Allah ya gafarta masa.

Sai dai gwamnan ya ki yin ƙarin haske game da yadda aka bi wajen kuɓutar da ɗaliban, inda ya dage akan cewar bayanin ba shi da mahimmanci.

A cewarsa, abinda keda muhimmanci shi ne gwamnati ta yi nasarar dukkanin ɗaliban ba tare da illata ko guda daga cikinsu ba.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa - Dauda Lawal 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like