Connect with us

Jan hankali

Fashin baƙi kan batun ƙirkiro ‘yan sandan jihohi a Najeriya – Barista Bulama Bukarti

Published

on

Masana harkokin tsaro a Najeriya su ce akwai fargaba kan batun neman kirkiro ‘yan sandan jihohi lura da yadda lamura ke tafiya da kuma tarin kalubale ko matsaloli da ka iya biyo baya.

Masanan suna wannan tsokaci ne bayan da kungiyar gwamnonin arewacin kasar da kuma majalisar sarakuna suka yi kiran da a samar da ‘yan sandan jiha, domin taimakawa wajen tunkarar matsalar tsaron da ake fuskanta a yankin.

Kafin wannan lokaci, jihohin kudancin kasar ne ke kan gaba wajen fafutukar ganin an samar da ‘yan sandan jiha, yayin da jihohin arewacin Najeriyar ba sa goyon bayan hakan.

Sai dai bayan kammala wani taro da gwamnonin arewan suka yi a farkon makon nan, sun nuna bukatar a samar da ‘yan sandan a matakin jiha al’amarin da masana ke ganin na tattare da fargaba.

Barista Bulama Bukarti babban jami’i ne a cibiyar kawo sauyi a kasashen duniya ta, Tony Blair da ke London, ya ce duk da cewa halin tabarbarewar tsaron kasar ne ya bar shugabannin arewa cikin yanayi na rashin zabi akwai abin dubawa sosai.

Bulama Bukarti ya ce babu shaka an jima ana wannan kiraye-kiraye, amma da ya ke yanzu tura ta kai bango, kusan babu zabi ne a yanzu.

Ya ce kirkiro ‘yan sanda ba wai abu ne mai wahala ba, kawai zaman gyara kudin tsarin Mulki ne.

Sai dai a wannan yanayi abin zai kasance ne kamar gaba kura baya sayaki, saboda idan aka yi duba kusan duk abubuwan da kudin tsarin Mulki ya bai wa gwamnoni, harkokin ba wai sun inganta ba ne ko sun zarta na gwamnatin tarayya.

Ya bada misali da asibitocin jihohi, da makarantu da sauran abubuwan da kudin tsarin Mulki ya bai wa gwamnoni damar samarwa amma abubuwa ba su inganta ba.

Wannan dalili ya sanya Bulama Bukarti ke ganin koda an bai wa jihohi damar kirkirar ta su rundunar ‘yan sanda ba lallai lamura su inganta.

‘’Ko kadan gwamnoni ba su nuna wata alamar za su iya tafiyar da harkokin da ke hannusu cikin aminci ba fiye da gwamntin Tarayya’’.

Bulama Bukarti na ganin akwai fargabar idan aka bai wa gwamnonin ‘yan sanda a hannusu, domin za su yi amfanin da damar wajen cusgunawa duk wadanda basa so musamman abokan hamayyar siyasa, a cewarsa.Ya bada misali da batun hukumomin zaɓe na jihohi, yana mai cewa tun da aka sakarwa gwamnoni harkar, kusan babu wani wuri da za a ce gashi an yi zabe mai inganci.

Ya kuma ce idan har ya zama dole a yi ‘yan sanda jiha to dole a fitar da dokar da za ta yi bayyani dalla-dalla kan huruminsu da kuma ‘yan sanda tarayya.‘’Sannan akwai bukatar dole a ware iyakoki jihohi dalla-dalla saboda kaucewa artabu tsakanin ‘yan sanda jihohin’’.

Masanin ya kuma ce dole makamansu ya kasance yana ƙarƙashin shugaban ƙasa ko gwamnatin tarayya, ta yada wani gwamna ba zai iya shigo da makaman da suka zarta kima ba, har a iya samun masu kokarin ballewa daga Najeriya.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Fashin baƙi kan batun ƙirkiro ‘yan sandan jihohi a Najeriya – Barista Bulama Bukarti – LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

CBN

Jabun kuɗaɗe sun bazu a gari — CBN

Published

on

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ja hankalin ’yan Najeriya kan jabun takardun kuɗin ƙasar da ke yawo a cikin al’umma a sakamakon raɗe-raɗin da ake yaɗawa na ƙarancin tsabar kuɗi.

Kakakin CBN, Hakama Sidi Ali ta shawarci al’umma da su kasance masu lura ganin cewa masu jabun kuɗaɗe na amfani da su a matsayin kuɗin mota ko a wurin yin cefane da gidajen abinci sauransu.

Sanarwar ta CBN ta ce “Dokar CBN ta tanadi hukucin ɗaurin aƙalla shekaru biyar ga duk wanda ya buga jabun kuɗaɗe.

“CBN na aiki da hukumomin tsaro da na hada-hadar kuɗaɗe wajen ganowa da ƙwace jabun kuɗaɗe da kuma tsare masu buga su.” in ji jami’ar.

Daga nan sai ta umarci bankuna, ’yan canji da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗaɗe da su ɗauki matakan da suka dace wajen ganowa da kuma hana yaɗuwar jabun kuɗaɗe.

Ta ƙara da cewa, “ana ƙira ga jama’a su kai ƙarar duk wanda suka ga yana yin jabun kuɗaɗe ga ofishin yan sanda ko na CBN mafi kusa.

Continue Reading

EFCC

EFCC ta fitar da matakai takwas na kare kai daga masu damfara da katin ATM

Published

on

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zangon ƙasa a Nijeriya, EFCC ta koka kan yadda take yawan samun rahotanni na waɗanda aka cire wa kuɗi daga banki ba tare da saninsu ba kuma akasari ta ATM.

Hukumar ta ce akasarin ƴan damfarar sun fi samun bayanan jama’a ko katin ATM ɗin mutane a wuraren cirar kuɗi na ATM ko kuma masu POS.

EFCC ta yi gargaɗi kan cewa ƴan damfarar suna amfani da katin ATM na bankin mutumin da suke so su yaudara, bayan haka sukan je wurinsa da niyyar taimako idan ya shiga ruɗani a gaban ATM.

Hukumar ta ce ƴan damfarar kan yi sauri su yi wa kwastoman bankin musaya da katinsa bayan su haddace lambobin sirrinsa a lokacin da suke ƙoƙarin taimakonsa, wanda daga baya sai su cire kuɗin da ke asusun ajiyarsa.

Dangane da haka ne hukumar ta fitar da hanyoyi takwas waɗanda take ganin idan jama’a sun bi su za su samu kariya daga masu damfarar:

KU KUMA KARANTA: EFCC za ta gurfanar da sojojin saman Najeriya a kotu kan zargin damfara a intanet

  1. Akwai buƙatar ajiye kati a aminctaccen wuri. Duk lokacin da ka karɓi katinka bayan cire kuɗi, ka tabbata katinka ka karɓa ba wai wanda ke kama da katinka ba.
  2. A rinƙa duba sauran kuɗin da ke asusu (balance) domin dubawa ko an cire kuɗi daga asusu.
  3. Saka ƙararrawa domin lura da duk wani abu da ya shafi asusun ajiya ko katin banki.
  4. Rufe lambobin da ake latsawa a jikin ATM ko POS da hannu a lokacin da ake saka lamobin sirri domin cire kuɗi ko wani amfani.
  5. A rinƙa neman taimako daga jami’an banki, ka da ka yi saurin biyan kuɗi ko cire kuɗi.
  6. A ƙira banki domin toshe katin ATM a duk lokacin da aka lura kati ya maƙale a cikin ATM ko kuma duk lokacin da aka lura da wani lamari wanda yake ba daidai ba.
  7. A tabbata an san lambar da za a iya toshe ATM da ita tare da amfani da ita cikin gaggawa a duk lokacin da aka ɓatar da katin ko aka sace shi.
  8. A latsa lambobin USSD na 966911# da kuma bin matakan da suka biyo baya domin toshe katin ATM nan take.
Continue Reading

Jan hankali

NUJ jihar Yobe, ta nuna rashin jin daɗi da ƙara farashi da masu gidajen mai suka yi

Published

on

Daga Ibraheem EL-TAFSEER

Ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar Yobe ta bayyana rashin jin daɗin ta game da halin rashin kishin ƙasa da wasu masu gidajen man fetur da ma’aikata suka yi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe da sauran ƙananan hukumomin jihar, dangane da ƙarancin man fetur da aka samu a yau da kuma ƙaruwar farashin mai ɗin, wanda hakan ya jawo dogon layi a gidajen man.

A wata takarda da ƙungiyar ta fitar, wanda shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Yobe, Kwamared Rajab Mohammed da sakatatensa Alhassan Sule Mamudo suka sa wa hanu, ta bayyana cewa, ƙungiyar ta damu matuƙa da halin da ‘yan jihar ke ciki masu son zaman lafiya.

KU KUMA KARANTA: Cire tallafin man fetur ya jawo hauhawar farashin mai a Najeriya

Don haka muna ƙira ga hukumomin tsaro, hukumomin gwamnati, hukumomin da abin ya shafa da duk masu ruwa da tsaki da su gaggauta ɗaukar matakan da suka dace don ganin an kawo karshen wannan mummunan yanayi da ke iya lalata tattalin arziƙin al’umma.

Za mu iya kwatanta shi a matsayin zagon ƙasa ga tsarin dimokuraɗiyyar Najeriya. Ƙungiyar za ta ci gaba da sanya ido kan lamarin tare da sanar da ‘yan ƙasar kan duk wani ci gaba mai kyau tare da yin ƙira ga kowa da kowa da su kwantar da hankula domin za a shawo kan lamarin cikin ruwan sanyi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like