Connect with us

'Yansanda

DARA TA CI GIDA: Mai safarar mutane ya kashe abokiyar aikinsa, tare da sayarda sassan jikinta

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Wani magidanci, Dauda Bello kuma shahararren mai safarar mutane, mai shekaru 50 a duniya, ya kashe wata mata ‘yar shekara 71, Messi Adisa tare da sayar Da Sassan Jikinta ga masu harkar tsafi.

“Abokiyar aikina ce a harkar fataucin yara kafin na kashe ta.” Ya shaida wa ‘yan sanda.

Jaridar P.M.EXPRESS ta rawaito cewa jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun ne suka yi nasarar kama wanda ake zargin mai suna Bello, inda aka kama shi dumu-dumu da laifin kashe marigayiya Messi Adisa, sannan ya sayar da wuya da idon sawunta ga wani matsafi, kafin bisani ya binne ta a asirce cikin wani kabari mara zurfi.

Sai dai bayan aikata wannan ɗanyan aikin, an kama shi kuma ya amsa laifin ake zarginsa da aikatawa, mummunan laifi da ke kai ga yiwa mutum hukuncin rai da rai a gidan kaso.

Jami’in hulda da jami’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, DSP Abimbola Oyeyemi ne ya tabbatar da hakan, ya bayyana cewa wanda ake zargin yana hannun ‘yan sanda ana yi masa tambayoyi tare da tsaurara bincike kan ayyukan ta’addancin da suka yi.

Da ake zantawa da shi, DSP Abimbola ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar Alhamis din da ta gabata.

DSP Abimbola ya bayyana cewa: “Bayan ɓacewar wadda aka kashe (dattijuwar), wadda aka gano ta bar gidanta a ranar 8 ga watan Yuni, ba ta dawo ba, hakan ya saka ‘yan uwanta korafi kan wacce ta batan.”

Bayan kama wanda ake zargin kuma ana yi masa tambayoyi, sai ya bayyana cewa ya dade da sanin wanda aka kashen, ya kuma bayyana cewa su biyun dukka ‘yan ƙungiyar harkar safarar yara ne.

Wanda ake zargin ya bayyana cewa “ya gayyaci wanda abin ya shafa zuwa gidansa ne a ranar kamar kullum, domin su tattauna harkokinsu na safara, amma da isa gidansa ya ga wani abu a tattare da ita wanda yake zargin maƙudan kudade ne.

Sakamakon haka ya bugi matar da sandar katako, domin ya karbi kudin daga hannun ta, wanda hakan ya sa ta suma, nan ya ɗauke ta zuwa daji, karshe ya kasheta ta hanyar.”

Wanda ake zargin ya bayyana cewa bayan ya caje jikin matar Naira  22,200 kawai ya gani, wanda ta karɓa ne matsayin kafin alƙalamin wani aiki. Bayan da ya gane cewa bai samu kudin da ya ke bida ba, sai ya yanke mata wuyan hannu da idon sawunta biyu, ya sayar da su ga wani matsafi domin ya sami ƙarin kudi.

Sai dai wanda ake zargin ya kai ‘yan sanda inda ya binne mamaciyar a wani kabari mara zurfi, an gano gawarta tare da kai ta wajen ajiyar gawa domin daukar rahoton gawar.

Abimbola ya bayyana cewa rundunar ‘yan sanda za ta gurfanar da duk wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya ta hanyar kama su tare da tuhumar su da laifin hada baki da kisan kai bayan kammala bincike.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like