Connect with us

Labarai

Dalilin da ya sa na wakilta su El-Rufai su amsa min tambayoyi a Chatham House – Tinubu

Published

on

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bayyana dalilin da ya sa ya wakilta wasu ‘ya’yan jam’iyyar su amsa masa tambayoyin da aka yi masa.
A cewar tsohon gwamnan na Legas, ya yi amfani da hanyar tawagarsa don nuna hadin gwiwa.

Tinubu ya yi magana ne a wurin laccar Chatham House mai taken: ‘Zaɓen Najeriya na 2023 a Landan.

A wajen laccar, Tinubu bayan jawabin buɗe taron, ya tura wa gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai tambayar da aka masa kan yadda gwamnatinsa (Tinubu) za ta magance matsalar rashin tsaro, ya kuma turawa daraktan yaɗa labarai na ƙungiyar yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Dele Aleke, tambayar da aka masa kan satar manfetir.

Tinubu ya kuma wakilta tsohon kwamishinan kuɗi a jihar Legas, Wale Edun, da ya amsa tambaya kan yadda shi (Tinubu) zai bunƙasa tattalin arzikin ƙasar idan aka zaɓe shi.

Sauran sun haɗa da shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila; tsohon gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi; Shugabar Mata ta APC ta Ƙasa, Dr Betta Edu; sun kuma amsa masa tambayoyin.

Tinubu ya ce: “Bari in nuna a nan ɗaya daga cikin falsafa da koyaswar da na yi imani da su sosai, shi ne yin haɗin gwiwa, idan an yi haɗin gwiwa a ƙungiyance ba za a iya rarrabuwa ba, don nuna hakan, zan ba da tambayoyin ga ƙungiyar.

“A bangaren ilimi kuwa, Tinubu ya yi alkawarin bayar da rance wa ɗaliɓai tare da gyara tsarin karatun Almajirai da ake yi a arewacin Najeriya.

El-Rufai wanda ya amsa tambayoyi kan harkokin tsaro, ya bayyana cewa, ‘yan fashi, ta’addanci, wariyar launin fata, da satar mai, na bukatar wani sabon salon da ya haɗa da kara yawan jami’an tsaro.

KU KUMA KARANTA:Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gudanar da taron gaggawa kan barazanar tsaro a birnin Abuja

“Dole ne adadin ya canza kuma gwamnatin Bola Tinubu ta riga ta yi wani tsari wanda aka sanya a cikin shirinmu na magance wannan, za mu ƙara yawan adadin sojojin Najeriya, za mu kara kaimi ba kawai adadin ba,da horo da kayan aiki,” in ji gwamnan Kaduna.

A nasa ɓangaren, Alake ya amsa tambayar kan yadda Tinubu ke shirin fitar da ‘yan Najeriya daga ƙangin talauci idan aka zaɓe shi da kuma daƙile satar mai cikin watanni shida.
“Babban manufarsa na bunƙasa ci gaban tattalin arziki shine, baiwa kamfanoni masubzaman kansu damar yin jarin da za su ƙara yawan aiki, bunkasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da kuma rage talauci,” in ji shi.

Har ila yau, Gbajabiamila ya amsa tambaya kan dabarun Tinubu kan tsaro, shugabar mata na jam’iyyar APC a matakin ƙasa ta amsa tambaya kan batun kiwon lafiya, da yadda za a mayar da magudanar kwakwalwa zuwa riba ga kasa da dai sauransu.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Zan yi adalci ga kowa, alƙawarin Tinubu ga ‘yan Najeriya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like