Connect with us

'Yansanda

Buhari ya yi tir da kashe basarake tareda mutanen ƙauye a Jihar Imo

Published

on

Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ya ba da umarnin gudanar da bincike kan kisan da aka yi wa Eze Asor, basaraken al’ummar Obudi-Agwa, da wasu mutum huɗu wadanda aka kashe mutanen ƙauyen, waɗanda suka rasa rayukansu a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari fadar sarkin da ke ƙaramar hukumar Oguta a jihar Imo.

Shugaba Buhari, a cikin wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Garba Shehu, ya fitar a ranar Talata ya yi tir da Allah wadai da harin tare da jajantawa iyalan waɗanda suka rasu.

Sanarwar ta ce, Shugaban ya umurci hukumomin tsaro a jihar da su tsananta bincike kan wannan aika-aika tare da tabbatar da cewa waɗanda suka yi aikata-aikar sun fuskanci fushin doka.

Yayin da yake jajantawa ‘yan uwa, abokan arziki, al’ummar Obudi-Agwa, da kuma duk waɗanda harin ya shafa, shugaban ya yi addu’ar Allah ya bai wa waɗanda suka jikkata sauƙi cikin gaggawa.

Shugaba Buhari ya yaba da irin ƙoƙarin da gwamnatin jihar Imo ke yi na inganta harkar tsaro, ya kuma ƙarfafa gwiwar ɗaukacin al’ummar Imo da ‘yan ƙasa da su bayar da goyon baya ga ƙoƙarin haɗin gwiwa na ‘yan jihar da sauran al’ummar yankin domin kiyaye kowa da kowa.”

A halin da ake ciki, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Imo, CSP Michael Abattam, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce nan take rundunar ta samu kiran gaggawa cewa wasu ‘yan bindiga da ake zargin mambobin haramtacciyar Ƙungiyar Biafra ne da kuma ƙungiyar ‘yan ta’addan ta, Eastern Security Network, sun far wa fadar basaraken.

Ya ce, Jami’in ‘yan sandan shiyya, tare da tawagar ‘yan sandan rundunar, nan take suka garzaya zuwa fadar, inda suka isa, aka gano cewa ‘yan bindigar sun gudu daga wurin.

“Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa ɓarayin sun zo ne a cikin motoci huɗu da babura biyu tare da wata mata inda suka yi kama da wadanda ke cikin halin kunci da suka zo suka kai masa rahoton wani lamari na gaggawa.

“Sarkin da bai yi tsammanin miyagu ba ne, sai ya ba su izinin shiga fadarsa, ya zauna da su, suna cikin bayyana dalilin ziyarar nasu, sai suka fito da bindigogi, suka harbe sarkin da mukarrabansa biyu, sannan suka yi gaggawar ficewa daga fadar.

“A kan hanyarsu ta zuwa ne suka kai hari ofishin ‘yan banga na Agwa, suka harbe mutum daya sannan suka tafi da babura uku.

“Jami’an ‘yan sanda ɗauke da bayanai daga shaidun gani da ido, sun bi hanyar da ‘yan bindigar suka tsere ne domin nemansu” inji shi.

Abattam ya ce an ajiye gawarwakin mamatan a ɗakin ajiyar gawarwaki, inda ya ƙara da cewa an yi wa al’ummar garin kariya da isassun jami’an ‘yan sanda.

Ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammed Barde, wanda ya yi Allah wadai da wannan danyen aikin, ya yi kira da a kwantar da hankula, inda ya ce rundunar ba za ta bar wani abu ba har sai an kama wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da fuskantar fushin doka akan su.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Published

on

Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta sanar da cafke wasu mutum biyu bisa zargin hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara.

Mai magana da yawun rundunar a Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce “muna tsare da mutum biyu kan lamarin, muna ci gaba da bincike.”

Tun farko, Kwamishinan tsaro na Jihar Katsina, Nasiru Mu’azu ya ce an sace dattijuwar ce a daren Juma’a a ƙauyen Kahutu da ke Karamar Hukumar Ɗanja.

Mu’azu ya ce waɗanda suka sace matar sun yi hakan ta hanyar bi ta bayan gida, inda suka sace ta ba tare da jami’an da ke tsaron gidan sun sani ba.

Ya kuma bayyana cewa tuni aka tura jami’an tsaro waɗanda suka bazama cikin dazuka domin bin sawun ’yan bindigar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Rarara

Neptune Prime Hausa ta ruwaito shaidu a kauyen sun ce da misalin karfe daya na dare ne dandazon ’yan bindiga suka kutsa gidan dattijuwar suka yi awon gaba da ita.

“A kafa suka zo, ba su yi harbi ba a lokacin da suka ka yi awon gaba da ita cikin ’yan mintoci.

“Dattijuwar ba ta bijire musu ba a lokacin da suka memi ta biyo su.

“Duk da cewa ’yan bindigar sun samu wasu mutane a gidan, amma mahaifiyar Rarara kaɗai suka ɗauka.

“Babu wani yunƙuri da aka yi na tunkarar ’yan bindigar a lokacin da suke tafiya da ita saboda bindigogin da suke ɗauke da su,” in ji wani mazaunin ƙauyen na Kahutu.
Ya ce, “Watakila maharan sun bar baburansu ne daga nesa suka tako zuwa cikin ƙauyen a kafa.

“Muna rokon Allah Ya kuɓutar da ita cikin koshin lafiya domin tana taimaka mana sosai a wannan ƙauyen.

“Danta Rarara mai yawan taimakon al’umma ne, kuma ya kawo mana abubuwan ci gaba sosai a garinmu,” in ji shi.

Continue Reading

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Published

on

'Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

‘Yan sanda sun kama kawali na ’yan bindiga

Daga Muhammad Kukuri 

Wani wanda yake kai wa ’yan bindiga karuwai domin yin lalata da su ya shiga hannun jami’an tsaro.

’Yan sanda sun bayyana cewa kawalin ya kuma ƙware wajen yin safarar makamai ga ƙungiyar jagoran ’yan bindiga mai suna Arɗo, wanda ake nema ruwa a jallo a yankin Kagarko da ke Jihar Kaduna.

An kuma gano cewa mutumin wanda yake harkar hada-hadar tura kuɗi ta PoS, shi ke kai wa iyalan ’yan bindiga kuɗaɗe a yankin na Kagarko.

Dubun kawalin ta cika ne a yayin wani samamen haɗin gwiwa da ’yan sanda suka gudanar a yankin.

Kwamishinan ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ya sanar ranar Talata cewa wanda ake zargin ya shaida musu cewa shi ke tsara yadda ake kai wa ’yan bindiga karuwai da miyagun ƙwayoyi da ma’aikatan lafiya a duk lokacin da suke buƙata.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a Kano sun kai mutanen da ake zargi da sayar da dala ba bisa ƙa’ida ba kotu

“Ya kuma amsa cewa yana yin dakon kuɗi tare da rabawa ga iyalan ’yan bindiga.

“A cewarsa, kuɗaɗen da ya raba wa iyalan ’yan bindiga sun haura Naira miliyan ashirin,” in ji kwamishinan ’yan sandan.

Igwe ya ce wanda ake zargin ya tabbatar musu cewa ’yan bindigar da ke ƙarƙashin Ardo sun kai 15 kowannensu da bindiga ƙirar AK-47.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like